• English
  • Business News
Tuesday, October 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?

by Sulaiman
4 months ago
Sin

An kammala taron shugabannin kamfanoni na kasa da kasa karo na 6 a birnin Qingdao na kasar Sin. A matsayin sa na muhimmin aikin raya tattalin arziki da cinikayya bisa matakin kasa irinsa na farko da kasar Sin ta kafa, musamman ga kamfanonin kasa da kasa, wannan taron ya janyo baki 570 daga kamfanonin kasa da kasa 465, na nahiyoyi 6 na duniya, wanda ya kai wani babban matsayi a tarihi.

Abun lura a nan shi ne, taron mai taken “kamfanonin kasa da kasa da kasar Sin- hada kan duniya da ci nasara tare”, ya nuna yadda kamfanonin kasa da kasa ke daukar kasar Sin a wani muhimmin matsayi yayin da suke tsara shirin gudanar da ayyukansu a duk fadin duniya.

  • Sin Ta Yi Matukar Allah Wadai Da Hare-Haren Da Amurka Ta Kaiwa Iran
  • Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Da Rasha Don Daukaka Amincewar Juna Ta Fuskar Siyasa Da Karfafa Muradun Juna

“Bosch yana bukatar kasar Sin, yana bukatar damar yin kirkire-kirkire da saurinsu a nan.” Kalaman shugaban reshen kamfanin Bosch na kasar Jamus dake kasar Sin Xu Daquan ke nan, inda ya bayyana ra’ayin bai daya na kamfanonin kasashen waje, wato yin nazari, da kirkire-kirkire a kasar Sin, matakin dake da muhimmanci a yayin da suke gudanar da harkokinsu a duniya. Ta hanyar yin cikakken amfani da kasuwa, da kwararru, da albarkatun kirkire-kirkire na kasar, za a kai ga ƙarfafa kwarewarsu ta yin takara a duniya.

Yanzu haka, ta hanyar kaddamar da jerin matakan samar da sauki da ba da hidima mai inganci a fannin zuba jari, kasar Sin na kokarin samar da muhalli mafi kyau ga kamfanonin kasashen waje don gudanar da harkokinsu. Yang Lan, babbar daraktar kamfanin Herbalife na kasar Amurka dake kula da harkokin Sin tana ganin cewa, ana ta samun kyautatuwar muhallin kasuwanci a kasar Sin. A cewarta, hakan ya karfafa gwiwarsu ta samun dauwamammen ci gaba a kasar Sin, da ma yin amfani da damammaki yadda ya kamata wajen yin takara.

Bisa irin kwarin gwiwar da suke samu, kamfanonin kasashen waje da ke Sin, suna gaggauta tsara shirin gudanar da harkoki a kasar. Kazalika, bisa yanayin da duniya ke ciki na kara tinkarar ra’ayin kashin kai, da kariyar ciniki, matakan da kamfanonin kasashen waje suke dauka sun nuna cewa, ta hanyar hadewa da kasar Sin ne kadai za su iya dunkulewa da duniya yadda ya kamata, kuma zuba jari a kasar Sin na nufin zuba jari a makomarsu ta nan gaba. (Mai fassara: Bilkisu Xin)

LABARAI MASU NASABA

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

October 13, 2025
Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta
Daga Birnin Sin

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

October 13, 2025
Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin
Daga Birnin Sin

Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin

October 13, 2025
Next Post
Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano - Janar Mai Adda’u

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

October 14, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

October 14, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Jarida A Kan Hanyarsa Ta Zuwa Ɗaukar Horo A Kwara

‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Jarida A Kan Hanyarsa Ta Zuwa Ɗaukar Horo A Kwara

October 14, 2025
Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

October 14, 2025
Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

October 13, 2025
Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

October 13, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

October 13, 2025
Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

October 13, 2025
NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3

NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3

October 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Gangamin Wayar Da Kai Kan Laifuka A Intanet

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Gangamin Wayar Da Kai Kan Laifuka A Intanet

October 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.