• English
  • Business News
Wednesday, July 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Nijeriya Ta Samu Ci Gaba Mai Inganci?

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Nijeriya Ta Samu Ci Gaba Mai Inganci?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A taron dandalin hadin gwiwar kasa da kasa karkashin shawarar Ziri Daya da Hanya Daya da ya gudana a birnin Beijing na kasar Sin a kwanan baya, Najeriya da kasar Sin sun zurfafa hadin gwiwarsu, inda suka kulla yarjejeniyoyin gudanar da wasu ayyuka, da darajarsu ta kai dalar Amurka biliyan 2, wadanda suka shafi zuba jari da wasu kamfanonin Sin za su yi a Najeriya, don gina masana’antun hada motoci masu amfani da wutar lantarki, da na’urorin da suke iya shawagi da ake kira “drone”, gami da batir na motoci, da dai sauransu. 

Ban da haka, wasu kamfanonin kasar Sin 10, sun bayyana niyyar zuba jari a Najeriya don raya wasu ayyukan da darajarsu ta kai dalar Amurka biliyan 4, wadanda suka shafi kera kayayyaki masu amfani da makamashin hasken rana, da kera motoci, da makamashi mai tsabta, da aikin gina yankin masana’antu, da na’urorin sarrafa iskar gas, da aikin koyar da fasahohin sana’o’i, da na’urorin samar da wutar lantarki masu inganci, da dai makamantansu.

  • Kasar Sin Ta Bukaci Tsagaita Wuta Da Samar Da Agajin Jin Kai A Zirin Gaza
  • An Yi Bikin Kaddamar Da Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Mutane Masu Bukata Ta Musamman Ta Asiya A Hangzhou

Bisa tantance wadannan ayyuka, za a iya ganin halayensu: Da farko, dukkansu sun shafi fasahohin zamani, da sabbin masana’antu masu kyakkyawar makoma. Na biyu, da yawa daga cikin ayyukan sun shafi yadda za a gina masana’antu da kayayyakin more rayuwa a Najeriya, kuma a tabbatar da mika fasahohi ga Najeriya, ta yadda ayyukan za su taimaki Najeriya wajen raya bangaren masana’antu. Na uku, a cikin ayyukan akwai hadin gwiwar da za a yi a fannonin koyar da ilimin sana’a, da kyautata fasahar samar da wutar lantarki, da raya tattalin arziki tare da kare muhalli, wadanda ke neman biyan bukatun Najeriya ta fuskar inganta zaman rayuwar jama’a. Wadannan halaye sun dace da taken taron Ziri Daya da Hanya Daya na wannan karo, na “aiwatar da shawarar Ziri Daya da Hanya Daya cikin inganci”.

Wannan take asalinsa shi ne ra’ayin “samun ci gaba mai inganci” na kasar Sin, wanda ya shafi kokarin kirkiro sabbin fasahohi, da inganta harkoki, da kare muhalli, gami da horar da ma’aikata, don neman samun ci gaba mai inganci, da sabbin fasahohi, da kyawun muhalli, da jin dadin zaman rayuwa, ta yadda za ta tabbatar da ci gaban tattalin arziki, da na al’umma mai dorewa.

Wannan ra’ayi ya riga ya zama wata muhimmiyar manufar kasar Sin a fannonin raya tattalin arziki, da gudanar da sauran ayyuka. Yanzu kasar Sin na neman yin amfani da shi wajen inganta hadin gwiwarta da sauran kasashe, da haifar musu da ci gaba, da zamanantarwa masu inganci.

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Mika Sakon Ta’aziyya Zuwa Ga Takwaransa Na Najeriya Bisa Rasuwar Muhammadu Buhari

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

Sai dai me ya sa kasar Sin ke son raba ilimi da dabaru, da fasahohi masu muhimmanci tare da sauran kasashe? Me ya sa take iya nuna cikakken sahihanci, a kokarinta na taimakawa Najeriya da sauran kasashen dake nahiyar Afirka samun ci gaba? Amsa ga wadannan tambayoyi ta shafi tsarin siyasa na kasar Sin.

Kasar Sin kasa ce mai rungumar tsarin siyasa na Gurguzu, hakan ya tabbatar da cewa, ba za ta yi kama da kasashen yammacin duniya ba, wadanda ke dogaro kan jari, da barin jarinsu ya yi tasiri yadda ya ga dama.

Manyan ‘yan kasuwa masu jari a hannunsu na kasashen yamma, suna son yin babakere a bangarorin fasahohi, da kudi, da tamburan kayayyaki, da shawo kan tsarin samar da kayayyaki, ta yadda za su samu karfin kare wani tsarin dake amfaninsu a duniya, don tabbatar da samun mafi yawan moriya. Wannan shi ne dalilin da ya sa kasashe masu tasowa gamuwa da wahalhalu yayin da suke neman raya tattalin arziki, a karkashin wani tsarin tattalin arziki na kasa da kasa da su kasashen yamma ke jagoranta.

A nata bangare, gwamnatin kasar Sin tana taka tsan-tsan game da illar da jari zai iya haddasawa ta rashin daidaito tsakanin al’ummu da kasashe, kana kasar ta yi kokarin kawar da gibin da ake samu tsakaninsu, don tabbatar da ci gaban tattalin arziki, da na al’umma mai dorewa a duniyarmu.

Saboda haka, kasar Sin tana kokarin kawar da talauci, da kyautata zaman rayuwar jama’a a cikin gida, gami da neman samun daidaituwa, da hadin kai, da ci gaba tare a duniya, da gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makoma ta bai daya. Wannan shi ne dalilin da ya sa kasar Sin ke son ganin sauran kasashe, ciki har da Najeriya, sun samu ci gaba mai inganci. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaIsra'ilaSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Matashin Dan Kwallon Barcelona Guiu Mai Shekaru 17 Ya Jefa Kwallon Farko A Kungiyar

Next Post

Asalin Kungiyoyin Mayakan Hamas, Hizbullah Da Manufofinsu

Related

Xi Jinping Ya Mika Sakon Ta’aziyya Zuwa Ga Takwaransa Na Najeriya Bisa Rasuwar Muhammadu Buhari
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Ta’aziyya Zuwa Ga Takwaransa Na Najeriya Bisa Rasuwar Muhammadu Buhari

11 minutes ago
Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

19 hours ago
Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO
Daga Birnin Sin

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

21 hours ago
An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

21 hours ago
Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%
Daga Birnin Sin

Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

22 hours ago
Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

23 hours ago
Next Post
Asalin Kungiyoyin Mayakan Hamas, Hizbullah Da Manufofinsu

Asalin Kungiyoyin Mayakan Hamas, Hizbullah Da Manufofinsu

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Mika Sakon Ta’aziyya Zuwa Ga Takwaransa Na Najeriya Bisa Rasuwar Muhammadu Buhari

Xi Jinping Ya Mika Sakon Ta’aziyya Zuwa Ga Takwaransa Na Najeriya Bisa Rasuwar Muhammadu Buhari

July 16, 2025
An Fara Binciken Mutuwar Wasu Ɗalibai 2 A Makarantar Kwana A Kano

An Fara Binciken Mutuwar Wasu Ɗalibai 2 A Makarantar Kwana A Kano

July 16, 2025
Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili

Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili

July 16, 2025
Peter Obi Ya Kai Wa Iyalan Buhari Ziyarar Ta’aziyya

Peter Obi Ya Kai Wa Iyalan Buhari Ziyarar Ta’aziyya

July 16, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

Omokri Da Sarki Sun Soki Obi Saboda Rashin Halartar Jana’izar Buhari

July 16, 2025
Kotu Ta Wanke Fayose Daga Zargin Zambar Naira Biliyan 3.3

Kotu Ta Wanke Fayose Daga Zargin Zambar Naira Biliyan 3.3

July 16, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

July 16, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Yara 2 Sun Kuɓuta Bayan Shafe Shekaru 6 A Hannun Boko Haram A Borno

July 16, 2025
Kasa Da Wata Biyu Ya Bar Mulki, Shin Ko Buhari Ya Cika Wa ‘Yan Nijeriya Alkawarin Da Ya Yi Mu Su?

EU, Turkiyya Da Sauran Ƙasashe Sun Yi Ta’aziyyar Rasuwar Buhari

July 16, 2025
Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

July 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.