ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Nijeriya Ta Samu Ci Gaba Mai Inganci?

by CGTN Hausa
3 years ago
Sin

A taron dandalin hadin gwiwar kasa da kasa karkashin shawarar Ziri Daya da Hanya Daya da ya gudana a birnin Beijing na kasar Sin a kwanan baya, Najeriya da kasar Sin sun zurfafa hadin gwiwarsu, inda suka kulla yarjejeniyoyin gudanar da wasu ayyuka, da darajarsu ta kai dalar Amurka biliyan 2, wadanda suka shafi zuba jari da wasu kamfanonin Sin za su yi a Najeriya, don gina masana’antun hada motoci masu amfani da wutar lantarki, da na’urorin da suke iya shawagi da ake kira “drone”, gami da batir na motoci, da dai sauransu. 

Ban da haka, wasu kamfanonin kasar Sin 10, sun bayyana niyyar zuba jari a Najeriya don raya wasu ayyukan da darajarsu ta kai dalar Amurka biliyan 4, wadanda suka shafi kera kayayyaki masu amfani da makamashin hasken rana, da kera motoci, da makamashi mai tsabta, da aikin gina yankin masana’antu, da na’urorin sarrafa iskar gas, da aikin koyar da fasahohin sana’o’i, da na’urorin samar da wutar lantarki masu inganci, da dai makamantansu.

  • Kasar Sin Ta Bukaci Tsagaita Wuta Da Samar Da Agajin Jin Kai A Zirin Gaza
  • An Yi Bikin Kaddamar Da Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Mutane Masu Bukata Ta Musamman Ta Asiya A Hangzhou

Bisa tantance wadannan ayyuka, za a iya ganin halayensu: Da farko, dukkansu sun shafi fasahohin zamani, da sabbin masana’antu masu kyakkyawar makoma. Na biyu, da yawa daga cikin ayyukan sun shafi yadda za a gina masana’antu da kayayyakin more rayuwa a Najeriya, kuma a tabbatar da mika fasahohi ga Najeriya, ta yadda ayyukan za su taimaki Najeriya wajen raya bangaren masana’antu. Na uku, a cikin ayyukan akwai hadin gwiwar da za a yi a fannonin koyar da ilimin sana’a, da kyautata fasahar samar da wutar lantarki, da raya tattalin arziki tare da kare muhalli, wadanda ke neman biyan bukatun Najeriya ta fuskar inganta zaman rayuwar jama’a. Wadannan halaye sun dace da taken taron Ziri Daya da Hanya Daya na wannan karo, na “aiwatar da shawarar Ziri Daya da Hanya Daya cikin inganci”.

ADVERTISEMENT

Wannan take asalinsa shi ne ra’ayin “samun ci gaba mai inganci” na kasar Sin, wanda ya shafi kokarin kirkiro sabbin fasahohi, da inganta harkoki, da kare muhalli, gami da horar da ma’aikata, don neman samun ci gaba mai inganci, da sabbin fasahohi, da kyawun muhalli, da jin dadin zaman rayuwa, ta yadda za ta tabbatar da ci gaban tattalin arziki, da na al’umma mai dorewa.

Wannan ra’ayi ya riga ya zama wata muhimmiyar manufar kasar Sin a fannonin raya tattalin arziki, da gudanar da sauran ayyuka. Yanzu kasar Sin na neman yin amfani da shi wajen inganta hadin gwiwarta da sauran kasashe, da haifar musu da ci gaba, da zamanantarwa masu inganci.

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sai dai me ya sa kasar Sin ke son raba ilimi da dabaru, da fasahohi masu muhimmanci tare da sauran kasashe? Me ya sa take iya nuna cikakken sahihanci, a kokarinta na taimakawa Najeriya da sauran kasashen dake nahiyar Afirka samun ci gaba? Amsa ga wadannan tambayoyi ta shafi tsarin siyasa na kasar Sin.

Kasar Sin kasa ce mai rungumar tsarin siyasa na Gurguzu, hakan ya tabbatar da cewa, ba za ta yi kama da kasashen yammacin duniya ba, wadanda ke dogaro kan jari, da barin jarinsu ya yi tasiri yadda ya ga dama.

Manyan ‘yan kasuwa masu jari a hannunsu na kasashen yamma, suna son yin babakere a bangarorin fasahohi, da kudi, da tamburan kayayyaki, da shawo kan tsarin samar da kayayyaki, ta yadda za su samu karfin kare wani tsarin dake amfaninsu a duniya, don tabbatar da samun mafi yawan moriya. Wannan shi ne dalilin da ya sa kasashe masu tasowa gamuwa da wahalhalu yayin da suke neman raya tattalin arziki, a karkashin wani tsarin tattalin arziki na kasa da kasa da su kasashen yamma ke jagoranta.

A nata bangare, gwamnatin kasar Sin tana taka tsan-tsan game da illar da jari zai iya haddasawa ta rashin daidaito tsakanin al’ummu da kasashe, kana kasar ta yi kokarin kawar da gibin da ake samu tsakaninsu, don tabbatar da ci gaban tattalin arziki, da na al’umma mai dorewa a duniyarmu.

Saboda haka, kasar Sin tana kokarin kawar da talauci, da kyautata zaman rayuwar jama’a a cikin gida, gami da neman samun daidaituwa, da hadin kai, da ci gaba tare a duniya, da gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makoma ta bai daya. Wannan shi ne dalilin da ya sa kasar Sin ke son ganin sauran kasashe, ciki har da Najeriya, sun samu ci gaba mai inganci. (Bello Wang)

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

MASU ALAKA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Daga Birnin Sin

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
Daga Birnin Sin

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Next Post
Asalin Kungiyoyin Mayakan Hamas, Hizbullah Da Manufofinsu

Asalin Kungiyoyin Mayakan Hamas, Hizbullah Da Manufofinsu

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.