• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Kasashe Da Dama Suke Sha’awar Shiga Tsarin BRICS

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Me Ya Sa Kasashe Da Dama Suke Sha’awar Shiga Tsarin BRICS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugabannin kasashen BRICS wato Brazil, Rasha, Indiya, China da South Africa za su yi ganawa karo na 15 a kasar Afirka ta Kudu nan ba da dadewa ba, lamarin da ya jawo hankalin kasashen duniya, musamman ma kara shigar da kasashe cikin tsarin BRICS. 

An ruwaito bangaren Afirka ta Kudu na cewa, yanzu kasashe fiye da 40 suna fatan shiga tsarin na BRICS, wasu fiye da 20 daga cikinsu kuma sun gabatar da bukatarsu a hukumance. Anil Sooklal, wakilin musamman na Afirka ta Kudu mai kula da harkokin BRICS ya bayyana yayin da yake zantawa da wakilin CMG cewa, kasashe da dama sun bayyana fatansu na shiga tsarin na BRICS, lamarin da ya nuna cewa, kasashen duniya suna da imani kan yadda BRICS suke ba da jagora wajen daidaita batutuwan kasa da kasa. To, me ya sa haka?

  • Xi Jinping Ya Yabawa Dangantakar ‘Yan Uwantaka Dake Tsakanin Sin Da Afirka Ta Kudu

Idan muka yi bitar tarihin hadin gwiwar BRICS, za mu fahimci cewa, neman samun bunkasuwa shi ne mafi muhimmanci. Alkaluman da kamfanin Acorn Macro Consulting na kasar Ingila ya gabatar a watan Maris na bana sun shaida cewa, a shekarar 2022 da ta wuce, adadin jimillar tattalin arzikin kasashen BRICS ya wuce na kungiyar G7 cikin tattalin arzikin duniya.

Tsarin hadin gwiwar BRICS ya taka muhimmiyar rawa wajen ba da jagora kan yin hadin kan kasashe masu tasowa da kuma kara azama kan tafiyar da harkokin kasa da kasa. Kasashen na BRICS suna mutunta ikon mulkin kan juna, da muradun tsaro da raya kasa, suna kuma nuna adawa da siyasar fin karfi, da tunanin yakin cacar baki da yin fito-na-fito tsakanin kungiyoyi. Haka kuma, sun kafa cibiyar nazarin allurar rigakafin cututtuka ta BRICS, a kokarin yaki da cutar COVID-19 tare.

Kafofin yada labaru na kasashen duniya na ganin cewa, kasashen BRICS sun gabatar da sabon tunani da wayar da kan kasashen duniya dangane da sabuwar odar kasa da kasa, wadda ta sha bamban da odar kasashen duniya da ke karkashin laimar kasashen yammacin duniya. (Tasallah Yuan)

Labarai Masu Nasaba

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Gabatar Da Kokenta Ga Amurka, Japan, Koriya Ta Kudu Kan Sanarwar Camp David

Next Post

Sin Da Sauran Kasashen BRICS Sun Ba Da Rahoton Fadada Cinikayya Cikin Sauri A Watannin Janairu Zuwa Yuli

Related

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu
Daga Birnin Sin

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

10 hours ago
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili
Daga Birnin Sin

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

12 hours ago
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

12 hours ago
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

16 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

18 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

18 hours ago
Next Post
Sin Da Sauran Kasashen BRICS Sun Ba Da Rahoton Fadada Cinikayya Cikin Sauri A Watannin Janairu Zuwa Yuli

Sin Da Sauran Kasashen BRICS Sun Ba Da Rahoton Fadada Cinikayya Cikin Sauri A Watannin Janairu Zuwa Yuli

LABARAI MASU NASABA

Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

June 8, 2025
An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

June 8, 2025
Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.