ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Kasashe Da Dama Suke Sha’awar Shiga Tsarin BRICS

by CMG Hausa
3 years ago
BRICS

Shugabannin kasashen BRICS wato Brazil, Rasha, Indiya, China da South Africa za su yi ganawa karo na 15 a kasar Afirka ta Kudu nan ba da dadewa ba, lamarin da ya jawo hankalin kasashen duniya, musamman ma kara shigar da kasashe cikin tsarin BRICS. 

An ruwaito bangaren Afirka ta Kudu na cewa, yanzu kasashe fiye da 40 suna fatan shiga tsarin na BRICS, wasu fiye da 20 daga cikinsu kuma sun gabatar da bukatarsu a hukumance. Anil Sooklal, wakilin musamman na Afirka ta Kudu mai kula da harkokin BRICS ya bayyana yayin da yake zantawa da wakilin CMG cewa, kasashe da dama sun bayyana fatansu na shiga tsarin na BRICS, lamarin da ya nuna cewa, kasashen duniya suna da imani kan yadda BRICS suke ba da jagora wajen daidaita batutuwan kasa da kasa. To, me ya sa haka?

  • Xi Jinping Ya Yabawa Dangantakar ‘Yan Uwantaka Dake Tsakanin Sin Da Afirka Ta Kudu

Idan muka yi bitar tarihin hadin gwiwar BRICS, za mu fahimci cewa, neman samun bunkasuwa shi ne mafi muhimmanci. Alkaluman da kamfanin Acorn Macro Consulting na kasar Ingila ya gabatar a watan Maris na bana sun shaida cewa, a shekarar 2022 da ta wuce, adadin jimillar tattalin arzikin kasashen BRICS ya wuce na kungiyar G7 cikin tattalin arzikin duniya.

ADVERTISEMENT

Tsarin hadin gwiwar BRICS ya taka muhimmiyar rawa wajen ba da jagora kan yin hadin kan kasashe masu tasowa da kuma kara azama kan tafiyar da harkokin kasa da kasa. Kasashen na BRICS suna mutunta ikon mulkin kan juna, da muradun tsaro da raya kasa, suna kuma nuna adawa da siyasar fin karfi, da tunanin yakin cacar baki da yin fito-na-fito tsakanin kungiyoyi. Haka kuma, sun kafa cibiyar nazarin allurar rigakafin cututtuka ta BRICS, a kokarin yaki da cutar COVID-19 tare.

Kafofin yada labaru na kasashen duniya na ganin cewa, kasashen BRICS sun gabatar da sabon tunani da wayar da kan kasashen duniya dangane da sabuwar odar kasa da kasa, wadda ta sha bamban da odar kasashen duniya da ke karkashin laimar kasashen yammacin duniya. (Tasallah Yuan)

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

 

 

BRICS
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Next Post
Sin Da Sauran Kasashen BRICS Sun Ba Da Rahoton Fadada Cinikayya Cikin Sauri A Watannin Janairu Zuwa Yuli

Sin Da Sauran Kasashen BRICS Sun Ba Da Rahoton Fadada Cinikayya Cikin Sauri A Watannin Janairu Zuwa Yuli

LABARAI MASU NASABA

Yaya Toure Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai

Yaya Toure Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai

September 9, 2026
Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa

Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa

September 9, 2026
’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.