• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Kasashen Afirka Suke Ta Korar Sojojin Kasashen Yamma?

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Me Ya Sa Kasashen Afirka Suke Ta Korar Sojojin Kasashen Yamma?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ana ta kara samun kasashen Afirka da suke korar sojojin kasashen yamma a ‘yan kwanakin nan. A jawaban taya murnar shiga sabuwar shekara ta 2025 da shugabannin kasashen Cote d’Ivoire da Senegal suka gabatar a kwanan nan, baki dayan shugabannin biyu sun bukaci kasar Faransa da ta janye sojojinta daga kasashensu, wato daga shekarar nan ta 2025. Idan ba mu manta ba, tuni kasashen Faransa da Amurka da Jamus suka janye sojojinsu daga kasashen Mali da Burkina Faso da kuma Nijer, bisa bukatar gwamnatocin rikon kwarya na kasashen. Kasar Chadi ma a watan Disamban bara ta bukaci Faransa da ta janye sojojinta daga kasar kafin ranar 31 ga watan Janairun bana. 

To, amma me ya sa kasashen Afirka suke ta korar sojojin kasashen yamma? 

Muna iya gano amsar tambayar daga zancen shugaban kasar Senegal Bassirou Diomaye Faye a yayin da yake tattaunawa tare da manema labarai a watan Nuwamban da ya gabata, inda ya ce, kasar Senegal ta cika shekaru 64 da samun ‘yancin kanta, don haka ita kasa ce mai mulkin kai, kuma kasar da ke da ‘yancin mulkin kanta ba za ta iya hakuri da kasancewar sansanin soji na Faransa a cikinta ba.

A shekarar 2011, bisa jagorancin kasashen Amurka da Faransa, kungiyar tsaro ta NATO ta dauki matakan soja na tsawon watanni 7 a kasar Libya domin hambarar da tsohon shugaban kasar Muammar Gaddafi, matakin da daga bisani ya haifar da tashe-tashen hankula a yankunan da ke makwabtaka da Libya, kuma a sabili da haka, aka samu yawaitar sumogar ta makamai da ma kafuwar kungiyoyin ‘yan ta’adda.

Daga baya, a shekarar 2013, Amurka da Faransa da ma sauran kasashen yamma suka fara tura sojojinsu zuwa Nijer da Burkina Faso da Chadi da Mali da sauran wasu kasashen da ke yankin Sahel, da sunan yakar kungiyoyi masu tsattsauran ra’ayi. Sai dai, hakan bai haifar da da mai ido ba, ganin yadda kasashen suka yi ta fama da karuwar talauci da rikice-rikice. Abin da ya sa karin al’ummar kasashen Afirka suka gane cewa, don yin katsalandan cikin harkokin gidansu, da kwace albarkatunsu ne, kasashen yamma suke girke sojojinsu, dalilin haka suka fara yi musu tutsu da nuna kin jinin sojojin.

Labarai Masu Nasaba

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

“Ko a yankunan da aka girke sojojin Faransa, ’yan ta’adda na ci gaba da kai hare-hare ga fararen hula. Ke nan, mece ce ma’anar kasancewarsu idan sun kasa kiyaye tsaro?” in ji Michael Ndimancho, wani shehun malami na kasar Kamaru.

Haka nan, wani marubucin kasar Nijer, Abdoulaye Sissoko ya yi nuni da cewa, burin da Amurka ke neman cimmawa shi ne tabbatar da ikonta a yankin kawai a maimakon yakar kungiyoyin ‘yan ta’adda.

Ban da haka, kasashen yamma sun taba yin mulkin mallaka ga akasarin kasashen Afirka, wadanda ko bayan da suka samu ‘yancin kansu, kasashen na yamma sun ci gaba da nuna babakere da neman tabbatar da ikonsu a kasashen. Wata mukalar da cibiyar nazarin tsare-tsare da harkokin kasa da kasa ta Amurka (CSIS) ta fitar ta yi nuni da cewa, kasashen Turai da Amurka kan dauki wasu matakai na tilasta wa kasashen Afirka bin turbar da suke so, matakin da a hakika yana nuna ci gaba da mulkin mullakarsu ne, wanda kuma tabbas yana haifar da talauci da koma baya ga kasashen Afirka da dama.

Tabbas, kasashen Afirka na farkawa. Kuma yadda kasashen ke korar sojojin kasashen yamma ya nuna aniyarsu ta neman ‘yancin kansu na hakika da kyamar sabon salon mulkin mallaka na kasashen yamma, kana abin da suke so shi ne tabbatar da zamantakewa ta daidai-wa-daida da hadin gwiwar cin moriyar juna da sauran kasashe.

Don haka, ya kamata kasashen yamma su gane cewa, lokacin yi wa kasashen Afirka duk abin da suka ga dama tuni ya wuce. Dole ne a bi ka’idar martaba juna, da zaman daidaito, da cin moriyar juna wajen aiwatar da hadin gwiwa da kasashen Afirka, sabo da ta haka ne za a kai ga tabbatar da ci gaba, da tsaro na bai daya.(Lubabatu Lei)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Akwai Buƙatar MDD Ta Shigo Don Binciko Masu Ɗaukar Nauyin Ta’addanci A Nijeriya Daga Ƙetare 

Next Post

Kasar Sin Za Ta Hada Hannu Da Kasashen Afirka Wajen Sa Kaimi Ga Zamanintarwa Mara Gurbata Muhalli

Related

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

4 hours ago
Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore
Ra'ayi Riga

Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

2 days ago
Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

5 days ago
Akwai Ma’ana Mai Zurfi A Bayan Da’a
Ra'ayi Riga

Akwai Ma’ana Mai Zurfi A Bayan Da’a

2 weeks ago
Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?
Ra'ayi Riga

Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?

2 weeks ago
Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya
Ra'ayi Riga

Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya

2 weeks ago
Next Post
Kasar Sin Za Ta Hada Hannu Da Kasashen Afirka Wajen Sa Kaimi Ga Zamanintarwa Mara Gurbata Muhalli

Kasar Sin Za Ta Hada Hannu Da Kasashen Afirka Wajen Sa Kaimi Ga Zamanintarwa Mara Gurbata Muhalli

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.