ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Kasashen Afirka Suke Ta Korar Sojojin Kasashen Yamma?

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Afirka

Ana ta kara samun kasashen Afirka da suke korar sojojin kasashen yamma a ‘yan kwanakin nan. A jawaban taya murnar shiga sabuwar shekara ta 2025 da shugabannin kasashen Cote d’Ivoire da Senegal suka gabatar a kwanan nan, baki dayan shugabannin biyu sun bukaci kasar Faransa da ta janye sojojinta daga kasashensu, wato daga shekarar nan ta 2025. Idan ba mu manta ba, tuni kasashen Faransa da Amurka da Jamus suka janye sojojinsu daga kasashen Mali da Burkina Faso da kuma Nijer, bisa bukatar gwamnatocin rikon kwarya na kasashen. Kasar Chadi ma a watan Disamban bara ta bukaci Faransa da ta janye sojojinta daga kasar kafin ranar 31 ga watan Janairun bana. 

To, amma me ya sa kasashen Afirka suke ta korar sojojin kasashen yamma? 

Muna iya gano amsar tambayar daga zancen shugaban kasar Senegal Bassirou Diomaye Faye a yayin da yake tattaunawa tare da manema labarai a watan Nuwamban da ya gabata, inda ya ce, kasar Senegal ta cika shekaru 64 da samun ‘yancin kanta, don haka ita kasa ce mai mulkin kai, kuma kasar da ke da ‘yancin mulkin kanta ba za ta iya hakuri da kasancewar sansanin soji na Faransa a cikinta ba.

ADVERTISEMENT

A shekarar 2011, bisa jagorancin kasashen Amurka da Faransa, kungiyar tsaro ta NATO ta dauki matakan soja na tsawon watanni 7 a kasar Libya domin hambarar da tsohon shugaban kasar Muammar Gaddafi, matakin da daga bisani ya haifar da tashe-tashen hankula a yankunan da ke makwabtaka da Libya, kuma a sabili da haka, aka samu yawaitar sumogar ta makamai da ma kafuwar kungiyoyin ‘yan ta’adda.

Daga baya, a shekarar 2013, Amurka da Faransa da ma sauran kasashen yamma suka fara tura sojojinsu zuwa Nijer da Burkina Faso da Chadi da Mali da sauran wasu kasashen da ke yankin Sahel, da sunan yakar kungiyoyi masu tsattsauran ra’ayi. Sai dai, hakan bai haifar da da mai ido ba, ganin yadda kasashen suka yi ta fama da karuwar talauci da rikice-rikice. Abin da ya sa karin al’ummar kasashen Afirka suka gane cewa, don yin katsalandan cikin harkokin gidansu, da kwace albarkatunsu ne, kasashen yamma suke girke sojojinsu, dalilin haka suka fara yi musu tutsu da nuna kin jinin sojojin.

LABARAI MASU NASABA

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Ga “Itacen Kuka” Na Kasar Sin

“Ko a yankunan da aka girke sojojin Faransa, ’yan ta’adda na ci gaba da kai hare-hare ga fararen hula. Ke nan, mece ce ma’anar kasancewarsu idan sun kasa kiyaye tsaro?” in ji Michael Ndimancho, wani shehun malami na kasar Kamaru.

Haka nan, wani marubucin kasar Nijer, Abdoulaye Sissoko ya yi nuni da cewa, burin da Amurka ke neman cimmawa shi ne tabbatar da ikonta a yankin kawai a maimakon yakar kungiyoyin ‘yan ta’adda.

Ban da haka, kasashen yamma sun taba yin mulkin mallaka ga akasarin kasashen Afirka, wadanda ko bayan da suka samu ‘yancin kansu, kasashen na yamma sun ci gaba da nuna babakere da neman tabbatar da ikonsu a kasashen. Wata mukalar da cibiyar nazarin tsare-tsare da harkokin kasa da kasa ta Amurka (CSIS) ta fitar ta yi nuni da cewa, kasashen Turai da Amurka kan dauki wasu matakai na tilasta wa kasashen Afirka bin turbar da suke so, matakin da a hakika yana nuna ci gaba da mulkin mullakarsu ne, wanda kuma tabbas yana haifar da talauci da koma baya ga kasashen Afirka da dama.

Tabbas, kasashen Afirka na farkawa. Kuma yadda kasashen ke korar sojojin kasashen yamma ya nuna aniyarsu ta neman ‘yancin kansu na hakika da kyamar sabon salon mulkin mallaka na kasashen yamma, kana abin da suke so shi ne tabbatar da zamantakewa ta daidai-wa-daida da hadin gwiwar cin moriyar juna da sauran kasashe.

Don haka, ya kamata kasashen yamma su gane cewa, lokacin yi wa kasashen Afirka duk abin da suka ga dama tuni ya wuce. Dole ne a bi ka’idar martaba juna, da zaman daidaito, da cin moriyar juna wajen aiwatar da hadin gwiwa da kasashen Afirka, sabo da ta haka ne za a kai ga tabbatar da ci gaba, da tsaro na bai daya.(Lubabatu Lei)

Afirka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA
Afirka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin
  • Sulaiman
    Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya
  • Sulaiman
    Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara
  • Sulaiman
    Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

MASU ALAKA

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
Ga “Itacen Kuka” Na Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ga “Itacen Kuka” Na Kasar Sin

July 1, 2026
Shekaru 105 Na Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin: Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa Daga Kwarewar Ci Gaban Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Shekaru 105 Na Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin: Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa Daga Kwarewar Ci Gaban Kasar Sin

June 30, 2026
Next Post
Kasar Sin Za Ta Hada Hannu Da Kasashen Afirka Wajen Sa Kaimi Ga Zamanintarwa Mara Gurbata Muhalli

Kasar Sin Za Ta Hada Hannu Da Kasashen Afirka Wajen Sa Kaimi Ga Zamanintarwa Mara Gurbata Muhalli

LABARAI MASU NASABA

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.