ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Kasashen Afirka Suke Ta Korar Sojojin Kasashen Yamma?

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Afirka

Ana ta kara samun kasashen Afirka da suke korar sojojin kasashen yamma a ‘yan kwanakin nan. A jawaban taya murnar shiga sabuwar shekara ta 2025 da shugabannin kasashen Cote d’Ivoire da Senegal suka gabatar a kwanan nan, baki dayan shugabannin biyu sun bukaci kasar Faransa da ta janye sojojinta daga kasashensu, wato daga shekarar nan ta 2025. Idan ba mu manta ba, tuni kasashen Faransa da Amurka da Jamus suka janye sojojinsu daga kasashen Mali da Burkina Faso da kuma Nijer, bisa bukatar gwamnatocin rikon kwarya na kasashen. Kasar Chadi ma a watan Disamban bara ta bukaci Faransa da ta janye sojojinta daga kasar kafin ranar 31 ga watan Janairun bana. 

To, amma me ya sa kasashen Afirka suke ta korar sojojin kasashen yamma? 

Muna iya gano amsar tambayar daga zancen shugaban kasar Senegal Bassirou Diomaye Faye a yayin da yake tattaunawa tare da manema labarai a watan Nuwamban da ya gabata, inda ya ce, kasar Senegal ta cika shekaru 64 da samun ‘yancin kanta, don haka ita kasa ce mai mulkin kai, kuma kasar da ke da ‘yancin mulkin kanta ba za ta iya hakuri da kasancewar sansanin soji na Faransa a cikinta ba.

ADVERTISEMENT

A shekarar 2011, bisa jagorancin kasashen Amurka da Faransa, kungiyar tsaro ta NATO ta dauki matakan soja na tsawon watanni 7 a kasar Libya domin hambarar da tsohon shugaban kasar Muammar Gaddafi, matakin da daga bisani ya haifar da tashe-tashen hankula a yankunan da ke makwabtaka da Libya, kuma a sabili da haka, aka samu yawaitar sumogar ta makamai da ma kafuwar kungiyoyin ‘yan ta’adda.

Daga baya, a shekarar 2013, Amurka da Faransa da ma sauran kasashen yamma suka fara tura sojojinsu zuwa Nijer da Burkina Faso da Chadi da Mali da sauran wasu kasashen da ke yankin Sahel, da sunan yakar kungiyoyi masu tsattsauran ra’ayi. Sai dai, hakan bai haifar da da mai ido ba, ganin yadda kasashen suka yi ta fama da karuwar talauci da rikice-rikice. Abin da ya sa karin al’ummar kasashen Afirka suka gane cewa, don yin katsalandan cikin harkokin gidansu, da kwace albarkatunsu ne, kasashen yamma suke girke sojojinsu, dalilin haka suka fara yi musu tutsu da nuna kin jinin sojojin.

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

“Ko a yankunan da aka girke sojojin Faransa, ’yan ta’adda na ci gaba da kai hare-hare ga fararen hula. Ke nan, mece ce ma’anar kasancewarsu idan sun kasa kiyaye tsaro?” in ji Michael Ndimancho, wani shehun malami na kasar Kamaru.

Haka nan, wani marubucin kasar Nijer, Abdoulaye Sissoko ya yi nuni da cewa, burin da Amurka ke neman cimmawa shi ne tabbatar da ikonta a yankin kawai a maimakon yakar kungiyoyin ‘yan ta’adda.

Ban da haka, kasashen yamma sun taba yin mulkin mallaka ga akasarin kasashen Afirka, wadanda ko bayan da suka samu ‘yancin kansu, kasashen na yamma sun ci gaba da nuna babakere da neman tabbatar da ikonsu a kasashen. Wata mukalar da cibiyar nazarin tsare-tsare da harkokin kasa da kasa ta Amurka (CSIS) ta fitar ta yi nuni da cewa, kasashen Turai da Amurka kan dauki wasu matakai na tilasta wa kasashen Afirka bin turbar da suke so, matakin da a hakika yana nuna ci gaba da mulkin mullakarsu ne, wanda kuma tabbas yana haifar da talauci da koma baya ga kasashen Afirka da dama.

Tabbas, kasashen Afirka na farkawa. Kuma yadda kasashen ke korar sojojin kasashen yamma ya nuna aniyarsu ta neman ‘yancin kansu na hakika da kyamar sabon salon mulkin mallaka na kasashen yamma, kana abin da suke so shi ne tabbatar da zamantakewa ta daidai-wa-daida da hadin gwiwar cin moriyar juna da sauran kasashe.

Don haka, ya kamata kasashen yamma su gane cewa, lokacin yi wa kasashen Afirka duk abin da suka ga dama tuni ya wuce. Dole ne a bi ka’idar martaba juna, da zaman daidaito, da cin moriyar juna wajen aiwatar da hadin gwiwa da kasashen Afirka, sabo da ta haka ne za a kai ga tabbatar da ci gaba, da tsaro na bai daya.(Lubabatu Lei)

Afirka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Afirka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina Kasa

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Kasar Sin Za Ta Hada Hannu Da Kasashen Afirka Wajen Sa Kaimi Ga Zamanintarwa Mara Gurbata Muhalli

Kasar Sin Za Ta Hada Hannu Da Kasashen Afirka Wajen Sa Kaimi Ga Zamanintarwa Mara Gurbata Muhalli

LABARAI MASU NASABA

Afirka

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Afirka

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.