• English
  • Business News
Tuesday, August 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Ministan Wajen Sin Kan Ziyarci Nahiyar Afirka A Duk Farkon Shekara?

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Me Ya Sa Ministan Wajen Sin Kan Ziyarci Nahiyar Afirka A Duk Farkon Shekara?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shigarmu sabuwar shekara ta 2025 ke da wuya, ministan harkokin wajen kasar Sin, Wang Yi, ya fara ziyara a nahiyar Afirka. A jiya ya isa kasar Namibia, daga baya zai kuma ziyarci kasashen Congo Brazaville, da Chadi, gami da tarayyar Najeriya. Hakika yadda ministan waje na kasar Sin kan yi ziyararsa ta farko a duk sabuwar shekara a nahiyar Afirka, ya riga ya zama al’adar kasar Sin ta fannin diplomasiyya, wadda ba a taba dakatarwa ba tsawon shekaru 35 da suka wuce.

Sai dai mene ne dalilin da ya sa aka dauki wannan manufa? Wang Yi, ministan wajen kasar Sin ya ba da amsa jiya, yayin da yake ganawa da shugabar kasar Namibia mai jiran gado, Netumbo Ndaitwah. A bayaninsa, kasar Sin ta dauki matakin ne saboda yadda take ba zumunci mai karfi a tsakanin bangarorin Sin da Afirka muhimmanci. Ban da haka, kasar na son nuna wa duniya cewa, duk wani yanayin da ake ciki, ita aminiyar kasashen Afirka ce, da za su iya dogaro a kanta, kuma za ta goyi bayansu a dandalin siyasar kasa da kasa a ko da yaushe.

  • An Rantsar Da Sabon Shugaban Ƙasar Ghana, John Mahama
  • Gwamnatin Sakkwato Ta Yi Alƙawarin Tallafa Wa Waɗanda Gobara Ta Shafa A Kasuwar Kara

Bugu da kari, za a ga yadda maganar jami’in na Sin ta samu shaida daga zancen tsohon shugaban kasar Najeriya, Olusegun Obasanjo. Yayin da yake hira da manema labaru a garin Abeokuta a kwanan nan, Mista Obasanjo ya ce kasar Sin ”babbar aminiyar hadin gwiwa ce”. A cewarsa, huldar dake tsakanin Afirka da Sin tana amfanar da junansu, kana kasar Sin tana kyakkyawar rawa wajen kiyaye adalci. Sa’an nan, an kulla huldar hadin gwiwa tsakanin Najeriya da Sin ne bisa tushen girmama juna, da rabon daidai-wa-daida, saboda haka huldar na da makoma mai haske.

To, bayan karanta kalaman Mista Wang Yi, da na Mista Obasanjo, watakila kai mai karatu za ka so ka yi tambayar cewar, mene ne tushen zumunci da huldar hadin gwiwa tsakanin Afirka da Sin? To, a ganina, asalin tushe mai muhimmanci kan lamarin shi ne akidar diflomasiyya ta kasar Sin, wato gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai-daya. Shugaba Xi Jinping na kasar Sin ne ya gabatar da wannan akida, wadda ta jaddada muhimmancin huldar dogaro da juna tsakanin kasashe daban daban, da kare moriyarsu ta bai-daya, da samun ci gaban tattalin arziki mai dorewa, gami da kulawa da al’amuran duniya cikin adalci. Kana akidar ta bukaci a lura da moriya da damuwar sauran kasashe, da kokarin tabbatar da ci gaban mabambantan kasashe na bai-daya.

Asalin akidar gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya shi ne tunanin gargajiya na Sinawa, kamar su ”neman tabbatar da jituwa a duniya” da ”darajanta zaman lafiya”, gami da ”mai da adalci a gaban moriyar kashin kai”. Ban da haka, akidar ta dace da babbar manufar jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, mai mulki a kasar, ta kuma yi kokarin tabbatar da jin dadin jama’a, da ci gaban harkokin dan Adam. Kana ita ce sabuwar dabarar da kasar Sin ta kirkiro don daidaita matsalolin da duniya ke fuskanta.

Labarai Masu Nasaba

Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu

Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?

Tsohuwar dabarar da kasashen yamma kan yi amfani da ita wajen wanzar da tsarin duniya, ita ce sanya kowa ya shiga takara da juna bisa bukatar kare moriyar kai, har zuwa lokacin da aka samu wani yanayi na daidaituwa. Sai dai tsohuwar dabarar ta kasa biyan bukatun dan Adam na tinkarar dimbin kalubaloli a wannan zamanin da muke ciki, abin da ya sa ake samun yawaitar tashe-tashen hankula a wurare daban daban. Saboda haka ana bukatar wata sabuwar dabara. Wannan bukata ta sa aka samu akidar gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai-daya.

Kasar Sin da kasashen Afirka suna aiwatar da akidar daga fannoni 2. Na farko, shi ne hadin gwiwarsu ya nuna yadda suke kokarin kare moriyar bai-daya, da neman samun ci gaba tare. Kana na biyu shi ne, hadin gwiwar Sin da Afirka na taka muhimmiyar rawa a fannonin kare hakkin kasashe masu tasowa, da adalci da daidaituwa a duniya, gami da wanzar da zaman lafiya da ci gaban tattalin arzikin kasashe daban daban.

A cewar Wang Yi, ministan harkokin wajen kasar Sin, wannan hulda a tsakanin Sin da Afirka ”ta dace da yanayi na adalci, da biyan bukatar dake akwai a zamanin da muke ciki, gami da taimakawa cika burin da al’ummar Sin da Afirka biliyan 2 da miliyan 800 suka sanya a gaba tare. ” (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NSCDC Ta Kama Wasu Mutane 7 Da Ake Zargi Da Laifin Sace Murafan Kwalbati A Abuja

Next Post

Awannin Da Sallamarsu A Matsayin Kwamishinoni, Gwamnan Bauchi Ya Naɗa 3 A Matsayin Mashawarta

Related

Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu
Ra'ayi Riga

Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu

4 days ago
Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?
Ra'ayi Riga

Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?

5 days ago
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe
Ra'ayi Riga

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

1 week ago
Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”
Ra'ayi Riga

Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”

2 weeks ago
Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna
Ra'ayi Riga

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

2 weeks ago
Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!
Ra'ayi Riga

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

3 weeks ago
Next Post
Bala Mohammed

Awannin Da Sallamarsu A Matsayin Kwamishinoni, Gwamnan Bauchi Ya Naɗa 3 A Matsayin Mashawarta

LABARAI MASU NASABA

An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami

An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami

August 12, 2025
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

Jagora A ADC Ya Ƙaryata Zargin Atiku Ya Kankane Komai A Jam’iyyar

August 12, 2025
’Yan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 6 A Taraba

’Yan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 6 A Taraba

August 12, 2025
Sadiq Umar Da Bello El-Rufai Sun Sayi Ƙungiyar Rancher Bees FC Ta Kaduna

Sadiq Umar Da Bello El-Rufai Sun Sayi Ƙungiyar Rancher Bees FC Ta Kaduna

August 12, 2025
Ba Iya Yunwa Ce Kaɗai Ke Kashe Ƙananan Yara A Katsina Ba – Gwamnati

Ba Iya Yunwa Ce Kaɗai Ke Kashe Ƙananan Yara A Katsina Ba – Gwamnati

August 12, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Batun Rashin Lafiyar Tinubu

August 12, 2025
Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

August 11, 2025
Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

August 11, 2025
An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK

An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK

August 11, 2025
Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli

Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli

August 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.