• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Ministan Wajen Sin Kan Ziyarci Nahiyar Afirka A Duk Farkon Shekara?

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Me Ya Sa Ministan Wajen Sin Kan Ziyarci Nahiyar Afirka A Duk Farkon Shekara?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shigarmu sabuwar shekara ta 2025 ke da wuya, ministan harkokin wajen kasar Sin, Wang Yi, ya fara ziyara a nahiyar Afirka. A jiya ya isa kasar Namibia, daga baya zai kuma ziyarci kasashen Congo Brazaville, da Chadi, gami da tarayyar Najeriya. Hakika yadda ministan waje na kasar Sin kan yi ziyararsa ta farko a duk sabuwar shekara a nahiyar Afirka, ya riga ya zama al’adar kasar Sin ta fannin diplomasiyya, wadda ba a taba dakatarwa ba tsawon shekaru 35 da suka wuce.

Sai dai mene ne dalilin da ya sa aka dauki wannan manufa? Wang Yi, ministan wajen kasar Sin ya ba da amsa jiya, yayin da yake ganawa da shugabar kasar Namibia mai jiran gado, Netumbo Ndaitwah. A bayaninsa, kasar Sin ta dauki matakin ne saboda yadda take ba zumunci mai karfi a tsakanin bangarorin Sin da Afirka muhimmanci. Ban da haka, kasar na son nuna wa duniya cewa, duk wani yanayin da ake ciki, ita aminiyar kasashen Afirka ce, da za su iya dogaro a kanta, kuma za ta goyi bayansu a dandalin siyasar kasa da kasa a ko da yaushe.

  • An Rantsar Da Sabon Shugaban Ƙasar Ghana, John Mahama
  • Gwamnatin Sakkwato Ta Yi Alƙawarin Tallafa Wa Waɗanda Gobara Ta Shafa A Kasuwar Kara

Bugu da kari, za a ga yadda maganar jami’in na Sin ta samu shaida daga zancen tsohon shugaban kasar Najeriya, Olusegun Obasanjo. Yayin da yake hira da manema labaru a garin Abeokuta a kwanan nan, Mista Obasanjo ya ce kasar Sin ”babbar aminiyar hadin gwiwa ce”. A cewarsa, huldar dake tsakanin Afirka da Sin tana amfanar da junansu, kana kasar Sin tana kyakkyawar rawa wajen kiyaye adalci. Sa’an nan, an kulla huldar hadin gwiwa tsakanin Najeriya da Sin ne bisa tushen girmama juna, da rabon daidai-wa-daida, saboda haka huldar na da makoma mai haske.

To, bayan karanta kalaman Mista Wang Yi, da na Mista Obasanjo, watakila kai mai karatu za ka so ka yi tambayar cewar, mene ne tushen zumunci da huldar hadin gwiwa tsakanin Afirka da Sin? To, a ganina, asalin tushe mai muhimmanci kan lamarin shi ne akidar diflomasiyya ta kasar Sin, wato gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai-daya. Shugaba Xi Jinping na kasar Sin ne ya gabatar da wannan akida, wadda ta jaddada muhimmancin huldar dogaro da juna tsakanin kasashe daban daban, da kare moriyarsu ta bai-daya, da samun ci gaban tattalin arziki mai dorewa, gami da kulawa da al’amuran duniya cikin adalci. Kana akidar ta bukaci a lura da moriya da damuwar sauran kasashe, da kokarin tabbatar da ci gaban mabambantan kasashe na bai-daya.

Asalin akidar gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya shi ne tunanin gargajiya na Sinawa, kamar su ”neman tabbatar da jituwa a duniya” da ”darajanta zaman lafiya”, gami da ”mai da adalci a gaban moriyar kashin kai”. Ban da haka, akidar ta dace da babbar manufar jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, mai mulki a kasar, ta kuma yi kokarin tabbatar da jin dadin jama’a, da ci gaban harkokin dan Adam. Kana ita ce sabuwar dabarar da kasar Sin ta kirkiro don daidaita matsalolin da duniya ke fuskanta.

Labarai Masu Nasaba

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba

Tsohuwar dabarar da kasashen yamma kan yi amfani da ita wajen wanzar da tsarin duniya, ita ce sanya kowa ya shiga takara da juna bisa bukatar kare moriyar kai, har zuwa lokacin da aka samu wani yanayi na daidaituwa. Sai dai tsohuwar dabarar ta kasa biyan bukatun dan Adam na tinkarar dimbin kalubaloli a wannan zamanin da muke ciki, abin da ya sa ake samun yawaitar tashe-tashen hankula a wurare daban daban. Saboda haka ana bukatar wata sabuwar dabara. Wannan bukata ta sa aka samu akidar gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai-daya.

Kasar Sin da kasashen Afirka suna aiwatar da akidar daga fannoni 2. Na farko, shi ne hadin gwiwarsu ya nuna yadda suke kokarin kare moriyar bai-daya, da neman samun ci gaba tare. Kana na biyu shi ne, hadin gwiwar Sin da Afirka na taka muhimmiyar rawa a fannonin kare hakkin kasashe masu tasowa, da adalci da daidaituwa a duniya, gami da wanzar da zaman lafiya da ci gaban tattalin arzikin kasashe daban daban.

A cewar Wang Yi, ministan harkokin wajen kasar Sin, wannan hulda a tsakanin Sin da Afirka ”ta dace da yanayi na adalci, da biyan bukatar dake akwai a zamanin da muke ciki, gami da taimakawa cika burin da al’ummar Sin da Afirka biliyan 2 da miliyan 800 suka sanya a gaba tare. ” (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NSCDC Ta Kama Wasu Mutane 7 Da Ake Zargi Da Laifin Sace Murafan Kwalbati A Abuja

Next Post

Awannin Da Sallamarsu A Matsayin Kwamishinoni, Gwamnan Bauchi Ya Naɗa 3 A Matsayin Mashawarta

Related

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

21 hours ago
Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba
Ra'ayi Riga

Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba

2 days ago
Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
Ra'ayi Riga

Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya

1 week ago
Bai Dace A Mika Wuya Ga Wanda Ya Nuna Fin Karfi Da Matakan Haraji Ba
Ra'ayi Riga

Bai Dace A Mika Wuya Ga Wanda Ya Nuna Fin Karfi Da Matakan Haraji Ba

2 weeks ago
Tabbas Amurka Za Ta Cije A Yakin Haraji Da Ta Kaddamar A Duniya
Ra'ayi Riga

Tabbas Amurka Za Ta Cije A Yakin Haraji Da Ta Kaddamar A Duniya

2 weeks ago
Illolin Da Manufar Haraji Kan Kayayyaki Ta Haifar A Kan Amerikawa
Ra'ayi Riga

Illolin Da Manufar Haraji Kan Kayayyaki Ta Haifar A Kan Amerikawa

2 weeks ago
Next Post
Bala Mohammed

Awannin Da Sallamarsu A Matsayin Kwamishinoni, Gwamnan Bauchi Ya Naɗa 3 A Matsayin Mashawarta

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.