ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Ministan Wajen Sin Kan Ziyarci Nahiyar Afirka A Duk Farkon Shekara?

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Sin

Shigarmu sabuwar shekara ta 2025 ke da wuya, ministan harkokin wajen kasar Sin, Wang Yi, ya fara ziyara a nahiyar Afirka. A jiya ya isa kasar Namibia, daga baya zai kuma ziyarci kasashen Congo Brazaville, da Chadi, gami da tarayyar Najeriya. Hakika yadda ministan waje na kasar Sin kan yi ziyararsa ta farko a duk sabuwar shekara a nahiyar Afirka, ya riga ya zama al’adar kasar Sin ta fannin diplomasiyya, wadda ba a taba dakatarwa ba tsawon shekaru 35 da suka wuce.

Sai dai mene ne dalilin da ya sa aka dauki wannan manufa? Wang Yi, ministan wajen kasar Sin ya ba da amsa jiya, yayin da yake ganawa da shugabar kasar Namibia mai jiran gado, Netumbo Ndaitwah. A bayaninsa, kasar Sin ta dauki matakin ne saboda yadda take ba zumunci mai karfi a tsakanin bangarorin Sin da Afirka muhimmanci. Ban da haka, kasar na son nuna wa duniya cewa, duk wani yanayin da ake ciki, ita aminiyar kasashen Afirka ce, da za su iya dogaro a kanta, kuma za ta goyi bayansu a dandalin siyasar kasa da kasa a ko da yaushe.

  • An Rantsar Da Sabon Shugaban Ƙasar Ghana, John Mahama
  • Gwamnatin Sakkwato Ta Yi Alƙawarin Tallafa Wa Waɗanda Gobara Ta Shafa A Kasuwar Kara

Bugu da kari, za a ga yadda maganar jami’in na Sin ta samu shaida daga zancen tsohon shugaban kasar Najeriya, Olusegun Obasanjo. Yayin da yake hira da manema labaru a garin Abeokuta a kwanan nan, Mista Obasanjo ya ce kasar Sin ”babbar aminiyar hadin gwiwa ce”. A cewarsa, huldar dake tsakanin Afirka da Sin tana amfanar da junansu, kana kasar Sin tana kyakkyawar rawa wajen kiyaye adalci. Sa’an nan, an kulla huldar hadin gwiwa tsakanin Najeriya da Sin ne bisa tushen girmama juna, da rabon daidai-wa-daida, saboda haka huldar na da makoma mai haske.

ADVERTISEMENT

To, bayan karanta kalaman Mista Wang Yi, da na Mista Obasanjo, watakila kai mai karatu za ka so ka yi tambayar cewar, mene ne tushen zumunci da huldar hadin gwiwa tsakanin Afirka da Sin? To, a ganina, asalin tushe mai muhimmanci kan lamarin shi ne akidar diflomasiyya ta kasar Sin, wato gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai-daya. Shugaba Xi Jinping na kasar Sin ne ya gabatar da wannan akida, wadda ta jaddada muhimmancin huldar dogaro da juna tsakanin kasashe daban daban, da kare moriyarsu ta bai-daya, da samun ci gaban tattalin arziki mai dorewa, gami da kulawa da al’amuran duniya cikin adalci. Kana akidar ta bukaci a lura da moriya da damuwar sauran kasashe, da kokarin tabbatar da ci gaban mabambantan kasashe na bai-daya.

Asalin akidar gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya shi ne tunanin gargajiya na Sinawa, kamar su ”neman tabbatar da jituwa a duniya” da ”darajanta zaman lafiya”, gami da ”mai da adalci a gaban moriyar kashin kai”. Ban da haka, akidar ta dace da babbar manufar jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, mai mulki a kasar, ta kuma yi kokarin tabbatar da jin dadin jama’a, da ci gaban harkokin dan Adam. Kana ita ce sabuwar dabarar da kasar Sin ta kirkiro don daidaita matsalolin da duniya ke fuskanta.

LABARAI MASU NASABA

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Tsohuwar dabarar da kasashen yamma kan yi amfani da ita wajen wanzar da tsarin duniya, ita ce sanya kowa ya shiga takara da juna bisa bukatar kare moriyar kai, har zuwa lokacin da aka samu wani yanayi na daidaituwa. Sai dai tsohuwar dabarar ta kasa biyan bukatun dan Adam na tinkarar dimbin kalubaloli a wannan zamanin da muke ciki, abin da ya sa ake samun yawaitar tashe-tashen hankula a wurare daban daban. Saboda haka ana bukatar wata sabuwar dabara. Wannan bukata ta sa aka samu akidar gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai-daya.

Kasar Sin da kasashen Afirka suna aiwatar da akidar daga fannoni 2. Na farko, shi ne hadin gwiwarsu ya nuna yadda suke kokarin kare moriyar bai-daya, da neman samun ci gaba tare. Kana na biyu shi ne, hadin gwiwar Sin da Afirka na taka muhimmiyar rawa a fannonin kare hakkin kasashe masu tasowa, da adalci da daidaituwa a duniya, gami da wanzar da zaman lafiya da ci gaban tattalin arzikin kasashe daban daban.

A cewar Wang Yi, ministan harkokin wajen kasar Sin, wannan hulda a tsakanin Sin da Afirka ”ta dace da yanayi na adalci, da biyan bukatar dake akwai a zamanin da muke ciki, gami da taimakawa cika burin da al’ummar Sin da Afirka biliyan 2 da miliyan 800 suka sanya a gaba tare. ” (Bello Wang)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

MASU ALAKA

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
Ra'ayi Riga

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Next Post
Bala Mohammed

Awannin Da Sallamarsu A Matsayin Kwamishinoni, Gwamnan Bauchi Ya Naɗa 3 A Matsayin Mashawarta

LABARAI MASU NASABA

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.