• English
  • Business News
Tuesday, June 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Shugabannin Kasa Da Kasa Da Manyan ‘Yan Kasuwa Suka Yi Ta Kawo Ziyara Kasar Sin?

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Me Ya Sa Shugabannin Kasa Da Kasa Da Manyan ‘Yan Kasuwa Suka Yi Ta Kawo Ziyara Kasar Sin?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daga ranar 18 zuwa 21 ga wata, shugaban kasar Gabon Ali Bango Ondimba ya kawo ziyarar aiki kasar Sin bisa gayyatar da aka yi masa, inda shugabannin kasashen biyu suka tsai da kudurin daga matsayin cikakkiyar dangantakar hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu, zuwa cikakkiyar dangantakar abokantaka ta hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare.

Shugaba Ali Bango ya kasance shugaba na farko daga nahiyar Afirka da kasar Sin ta karba a wannan shekara, haka kuma, yana daga cikin shugabannin kasashe da shiyyoyi da suka kawo ziyara kasar Sin cikin lokacin da bai kai wata daya ba, wato biyowa bayan ziyarar firaministocin Spaniya, da Malaysia da Singapore, da shugaban kasar Faransa, da shugabar tarayyar Turai, sai kuma shugaban kasar Brazil.

  • An Bude Bikin Fina-finai Na Kasa Da Kasa Na Beijing Karo Na 13

Ban da su kuma, kusan manyan jagororin kamfanonin kasa da kasa guda 100 da suka hada da Apple, da Mercedes-Benz, da makamantansu ma suka ziyarci kasar Sin, don neman damammaki na kasuwanci.

Amma me ya sa shugabannin kasa da kasa da manyan ‘yan kasuwa suka yi ta kawo ziyara kasar Sin? A yanayin da ake ciki na rashin samun kwanciyar hankali da kuma rashin tabbas, me ya sa kasashen duniya suka rika zura ido ga kasar Sin?
Domin amsa tambayoyin, za mu fara da yin nazari kan yanayin siyasar da ake ciki a duniya, inda yanzu haka ake fuskantar tashin hankali da sauye-sauye, inda kasashen yamma da ke karkashin jagorancin Amurka suka yi ta haifar da rarrabuwar kawuna, da yin fito-na-fito a tsakanin kasashen duniya, matakin da ya jawo damuwa da rashin jin dadi ga kasashe da dama. Kasar Sin a nata bangaren, tana ganin duniya ta ishi dukkanin kasashe su bunkasa kan su, kuma ta ba da shawarar kafa sabon salon dangantakar kasa da kasa mai girmama juna, da adalci, da hadin gwiwar cin moriyar juna, inda bi da bi, ta gabatar da manufar gina zaman al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya, da shawarar ziri daya da hanya daya, da shawarar raya duniya, da shawarar kiyaye tsaron duniya, da kuma shawarar wayin kai ta duniya, wadanda suke kunshe da tunanin gargajiya na kasar na rungumar zaman lafiya da kiyaye bambancin juna, wadanda kuma suka samu karbuwa daga akasarin kasashen duniya.

Shugaban kasar Gabon kafin ya fara wannan ziyara ma ya yaba da wadannan shawarwari da kasar Sin ya gabatar, yana mai cewa, shawarwarin za su taimaka ga kiyaye zaman lafiya da tsaro a duniya, tare da tabbatar da ci gaban kasa da kasa. Shi ma shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron a yayin ziyarar sa ya ce, Faransa na nacewa ga manufar diflomasiyya mai ‘yanci, kuma tana ganin ya kamata Turai ta kiyaye ‘yancinta ta fannin tsare-tsarenta, har wa yau ya bayyana rashin amincewa da jawo rarrabuwar kawuna, da yin fito-na-fito a tsakanin kasa da kasa.

Labarai Masu Nasaba

Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Ayyukan Kiwon Lafiya Kyauta Ga Yara A Botswana

Tawagar Likitocin Kasar Sin Sun Duba Marayu Marasa Lafiya Fiye Da 200 Kyauta A Zanzibar Ta Tanzaniya

A fannin tattalin arzikinta kuma, tun bayan da kasar Sin ta inganta matakan kandagarkin annobar Covid-19, tattalin arzikin kasar Sin ya farfado. Alkaluman da hukumar kididdiga ta kasar Sin ta samar da kwanan nan sun shaida cewa, a farkon watannin ukun bana, mizanin tattalin arziki na GDP na kasar ya kai yuan trilliyan 28499.7, wanda ya karu da kaso 4.5% bisa na makamancin lokacin bara, har ma hukumomin kasa da kasa da dama sun kyautata hasashensu kan bunkasuwar tattalin arzikin kasar cikin wannan shekara.

Kasancewarta kasa mafin karfin tattalin arziki na biyu a duniya, farfadowar tattalin arzikin kasar na amfanar duniya baki daya a maimakon ita kanta. Babbar darektar asusun ba da lamuni na duniya IMF, Kristalina Georgieva ta ce, farfadowar tattalin arzikin kasar Sin na nufin kasar Sin ka iya bayar da gudummawar da za ta kai kaso 1/3, ko ma fiye da haka ga ci gaban tattalin arzikin duniya a bana. Abu mafi muhimmanci kuma shi ne yadda kasar Sin ke nacewa ga kiyaye dunkulewar ci gaban duniya, da ma inganta bude kofarta ga ketare, ta yadda karin kasashen duniya za su ci gajiyar bunkasuwarta.

Daidai da yadda Ola Källenius, shugaban darektocin kamfanin Mercedes-Benz, wanda ya kawo ziyara kasar Sin kwanan baya ya fada, cewa “za mu ci gaba da zuba jari ga kasar Sin, kasancewar yadda kasar Sin na kiyaye bunkasuwarta, da bude kofarta ga ketare, ya samar da damammaki masu daraja gare mu.”

Har kullum kasar Sin na rungumar dunkulewar duniya baki daya, kuma tana fatan ganin bunkasuwar kasa da kasa ta bai daya. Ko a tabbatar da ‘yancin kai ta fannin siyasa, ko kuma a dogara ga wasu, ko a bude wa juna kofa ta fannin tattalin arziki, ko kuma a rika yin gaba da juna, duk kasa mai hankali za ta yi zabin da ya dace.(Lubabatu)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shawarar Kasar Sin Game Da Tsaron Kasa Da Kasa Ta Ingiza Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya, In Ji Masana

Next Post

Baba Buhari: Madugun Cin Bashi A Jamhuriya Ta Hudu

Related

Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Ayyukan Kiwon Lafiya Kyauta Ga Yara A Botswana
Daga Birnin Sin

Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Ayyukan Kiwon Lafiya Kyauta Ga Yara A Botswana

1 hour ago
Tawagar Likitocin Kasar Sin Sun Duba Marayu Marasa Lafiya Fiye Da 200 Kyauta A Zanzibar Ta Tanzaniya
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitocin Kasar Sin Sun Duba Marayu Marasa Lafiya Fiye Da 200 Kyauta A Zanzibar Ta Tanzaniya

2 hours ago
Za A Gudanar Da Taron Dandalin Davos Na Lokacin Zafi Karo Na 16 a Birnin Tianjin Na Sin
Daga Birnin Sin

Za A Gudanar Da Taron Dandalin Davos Na Lokacin Zafi Karo Na 16 a Birnin Tianjin Na Sin

3 hours ago
CMG Ya Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Kwamitin Shirya Gasar Wasannin Olympics Ta Milano Cortina Ta Shekarar 2026
Daga Birnin Sin

CMG Ya Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Kwamitin Shirya Gasar Wasannin Olympics Ta Milano Cortina Ta Shekarar 2026

4 hours ago
Binciken CGTN: Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kasa Da Kasa Sun Yi Allah Wadai Da Harin Amurka Kan Iran
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kasa Da Kasa Sun Yi Allah Wadai Da Harin Amurka Kan Iran

6 hours ago
Sin Na Fatan Kwamitin Sulhun MDD Zai Goyi Bayan Kuduri Game Da Halin Da Iran Ke Ciki
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Kwamitin Sulhun MDD Zai Goyi Bayan Kuduri Game Da Halin Da Iran Ke Ciki

8 hours ago
Next Post
Baba Buhari: Madugun Cin Bashi A Jamhuriya Ta Hudu

Baba Buhari: Madugun Cin Bashi A Jamhuriya Ta Hudu

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi

Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi

June 23, 2025
EFCC Ta Kama Tsohon Babban Jami’in NNPC Kan Zargin Satar Dala Biliyan 7.2

EFCC Ta Kama Tsohon Babban Jami’in NNPC Kan Zargin Satar Dala Biliyan 7.2

June 23, 2025
Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Ayyukan Kiwon Lafiya Kyauta Ga Yara A Botswana

Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Ayyukan Kiwon Lafiya Kyauta Ga Yara A Botswana

June 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gargaɗin Amurka: Gwamnati Ta Bayar Da Tabbaci Akwai Tsaro A Abuja

June 23, 2025
Tawagar Likitocin Kasar Sin Sun Duba Marayu Marasa Lafiya Fiye Da 200 Kyauta A Zanzibar Ta Tanzaniya

Tawagar Likitocin Kasar Sin Sun Duba Marayu Marasa Lafiya Fiye Da 200 Kyauta A Zanzibar Ta Tanzaniya

June 23, 2025
An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

June 23, 2025
Za A Gudanar Da Taron Dandalin Davos Na Lokacin Zafi Karo Na 16 a Birnin Tianjin Na Sin

Za A Gudanar Da Taron Dandalin Davos Na Lokacin Zafi Karo Na 16 a Birnin Tianjin Na Sin

June 23, 2025
CMG Ya Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Kwamitin Shirya Gasar Wasannin Olympics Ta Milano Cortina Ta Shekarar 2026

CMG Ya Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Kwamitin Shirya Gasar Wasannin Olympics Ta Milano Cortina Ta Shekarar 2026

June 23, 2025
Karin Kudin Mai: Hakika An Ci Amanarmu, In Ji ‘Yan Kwadago

NNPC Ya Ƙara Kuɗin Fetur, Duba Sabon Farashin

June 23, 2025
Binciken CGTN: Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kasa Da Kasa Sun Yi Allah Wadai Da Harin Amurka Kan Iran

Binciken CGTN: Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kasa Da Kasa Sun Yi Allah Wadai Da Harin Amurka Kan Iran

June 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.