• Leadership Hausa
Tuesday, December 5, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Shugabannin Kasa Da Kasa Da Manyan ‘Yan Kasuwa Suka Yi Ta Kawo Ziyara Kasar Sin?

by CMG Hausa
8 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Me Ya Sa Shugabannin Kasa Da Kasa Da Manyan ‘Yan Kasuwa Suka Yi Ta Kawo Ziyara Kasar Sin?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daga ranar 18 zuwa 21 ga wata, shugaban kasar Gabon Ali Bango Ondimba ya kawo ziyarar aiki kasar Sin bisa gayyatar da aka yi masa, inda shugabannin kasashen biyu suka tsai da kudurin daga matsayin cikakkiyar dangantakar hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu, zuwa cikakkiyar dangantakar abokantaka ta hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare.

Shugaba Ali Bango ya kasance shugaba na farko daga nahiyar Afirka da kasar Sin ta karba a wannan shekara, haka kuma, yana daga cikin shugabannin kasashe da shiyyoyi da suka kawo ziyara kasar Sin cikin lokacin da bai kai wata daya ba, wato biyowa bayan ziyarar firaministocin Spaniya, da Malaysia da Singapore, da shugaban kasar Faransa, da shugabar tarayyar Turai, sai kuma shugaban kasar Brazil.

  • An Bude Bikin Fina-finai Na Kasa Da Kasa Na Beijing Karo Na 13

Ban da su kuma, kusan manyan jagororin kamfanonin kasa da kasa guda 100 da suka hada da Apple, da Mercedes-Benz, da makamantansu ma suka ziyarci kasar Sin, don neman damammaki na kasuwanci.

Amma me ya sa shugabannin kasa da kasa da manyan ‘yan kasuwa suka yi ta kawo ziyara kasar Sin? A yanayin da ake ciki na rashin samun kwanciyar hankali da kuma rashin tabbas, me ya sa kasashen duniya suka rika zura ido ga kasar Sin?
Domin amsa tambayoyin, za mu fara da yin nazari kan yanayin siyasar da ake ciki a duniya, inda yanzu haka ake fuskantar tashin hankali da sauye-sauye, inda kasashen yamma da ke karkashin jagorancin Amurka suka yi ta haifar da rarrabuwar kawuna, da yin fito-na-fito a tsakanin kasashen duniya, matakin da ya jawo damuwa da rashin jin dadi ga kasashe da dama. Kasar Sin a nata bangaren, tana ganin duniya ta ishi dukkanin kasashe su bunkasa kan su, kuma ta ba da shawarar kafa sabon salon dangantakar kasa da kasa mai girmama juna, da adalci, da hadin gwiwar cin moriyar juna, inda bi da bi, ta gabatar da manufar gina zaman al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya, da shawarar ziri daya da hanya daya, da shawarar raya duniya, da shawarar kiyaye tsaron duniya, da kuma shawarar wayin kai ta duniya, wadanda suke kunshe da tunanin gargajiya na kasar na rungumar zaman lafiya da kiyaye bambancin juna, wadanda kuma suka samu karbuwa daga akasarin kasashen duniya.

Shugaban kasar Gabon kafin ya fara wannan ziyara ma ya yaba da wadannan shawarwari da kasar Sin ya gabatar, yana mai cewa, shawarwarin za su taimaka ga kiyaye zaman lafiya da tsaro a duniya, tare da tabbatar da ci gaban kasa da kasa. Shi ma shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron a yayin ziyarar sa ya ce, Faransa na nacewa ga manufar diflomasiyya mai ‘yanci, kuma tana ganin ya kamata Turai ta kiyaye ‘yancinta ta fannin tsare-tsarenta, har wa yau ya bayyana rashin amincewa da jawo rarrabuwar kawuna, da yin fito-na-fito a tsakanin kasa da kasa.

Labarai Masu Nasaba

Da Na Gaba Ake Gane Zurfin Ruwa

An Rufe Taron Fahimtar Sin Na shekarar 2023

A fannin tattalin arzikinta kuma, tun bayan da kasar Sin ta inganta matakan kandagarkin annobar Covid-19, tattalin arzikin kasar Sin ya farfado. Alkaluman da hukumar kididdiga ta kasar Sin ta samar da kwanan nan sun shaida cewa, a farkon watannin ukun bana, mizanin tattalin arziki na GDP na kasar ya kai yuan trilliyan 28499.7, wanda ya karu da kaso 4.5% bisa na makamancin lokacin bara, har ma hukumomin kasa da kasa da dama sun kyautata hasashensu kan bunkasuwar tattalin arzikin kasar cikin wannan shekara.

Kasancewarta kasa mafin karfin tattalin arziki na biyu a duniya, farfadowar tattalin arzikin kasar na amfanar duniya baki daya a maimakon ita kanta. Babbar darektar asusun ba da lamuni na duniya IMF, Kristalina Georgieva ta ce, farfadowar tattalin arzikin kasar Sin na nufin kasar Sin ka iya bayar da gudummawar da za ta kai kaso 1/3, ko ma fiye da haka ga ci gaban tattalin arzikin duniya a bana. Abu mafi muhimmanci kuma shi ne yadda kasar Sin ke nacewa ga kiyaye dunkulewar ci gaban duniya, da ma inganta bude kofarta ga ketare, ta yadda karin kasashen duniya za su ci gajiyar bunkasuwarta.

Daidai da yadda Ola Källenius, shugaban darektocin kamfanin Mercedes-Benz, wanda ya kawo ziyara kasar Sin kwanan baya ya fada, cewa “za mu ci gaba da zuba jari ga kasar Sin, kasancewar yadda kasar Sin na kiyaye bunkasuwarta, da bude kofarta ga ketare, ya samar da damammaki masu daraja gare mu.”

Har kullum kasar Sin na rungumar dunkulewar duniya baki daya, kuma tana fatan ganin bunkasuwar kasa da kasa ta bai daya. Ko a tabbatar da ‘yancin kai ta fannin siyasa, ko kuma a dogara ga wasu, ko a bude wa juna kofa ta fannin tattalin arziki, ko kuma a rika yin gaba da juna, duk kasa mai hankali za ta yi zabin da ya dace.(Lubabatu)

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shawarar Kasar Sin Game Da Tsaron Kasa Da Kasa Ta Ingiza Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya, In Ji Masana

Next Post

Baba Buhari: Madugun Cin Bashi A Jamhuriya Ta Hudu

Related

Da Na Gaba Ake Gane Zurfin Ruwa
Daga Birnin Sin

Da Na Gaba Ake Gane Zurfin Ruwa

8 hours ago
An Rufe Taron Fahimtar Sin Na shekarar 2023
Daga Birnin Sin

An Rufe Taron Fahimtar Sin Na shekarar 2023

8 hours ago
Gwamnatin Birtaniya Na Damuwa Kan Yadda Ake Neman A Mayar Da Kayayyakin Tarihi Da Ta Mallaka
Daga Birnin Sin

Gwamnatin Birtaniya Na Damuwa Kan Yadda Ake Neman A Mayar Da Kayayyakin Tarihi Da Ta Mallaka

10 hours ago
Babban Edita Dan Kasar Ghana: A Bayyana Yadda Sin Da Afirka Suke Hadin Gwiwa Da Juna
Daga Birnin Sin

Babban Edita Dan Kasar Ghana: A Bayyana Yadda Sin Da Afirka Suke Hadin Gwiwa Da Juna

10 hours ago
Jami’ar EDF: Matakan Lardin Guangdong Na Sin Kan Magance Sauyin Yanayi Abin Koyi Ne
Daga Birnin Sin

Jami’ar EDF: Matakan Lardin Guangdong Na Sin Kan Magance Sauyin Yanayi Abin Koyi Ne

12 hours ago
Xi Jinping Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron Kasa Da Kasa Na Congdu Na 2023
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron Kasa Da Kasa Na Congdu Na 2023

15 hours ago
Next Post
Baba Buhari: Madugun Cin Bashi A Jamhuriya Ta Hudu

Baba Buhari: Madugun Cin Bashi A Jamhuriya Ta Hudu

LABARAI MASU NASABA

Da Na Gaba Ake Gane Zurfin Ruwa

Da Na Gaba Ake Gane Zurfin Ruwa

December 4, 2023
An Rufe Taron Fahimtar Sin Na shekarar 2023

An Rufe Taron Fahimtar Sin Na shekarar 2023

December 4, 2023
Kotu Ta Umarci Dawo Da Motoci 50 Da Tsohon Gwamnan Zamfara Ya Kwashe

Kotu Ta Umarci Dawo Da Motoci 50 Da Tsohon Gwamnan Zamfara Ya Kwashe

December 4, 2023
Kasafin 2024 Ya Bada Fifiko Ne Wajen Jaddada Ajandar Saisaita Nijeriya – Minista

Kasafin 2024 Ya Bada Fifiko Ne Wajen Jaddada Ajandar Saisaita Nijeriya – Minista

December 4, 2023
Gwamnatin Birtaniya Na Damuwa Kan Yadda Ake Neman A Mayar Da Kayayyakin Tarihi Da Ta Mallaka

Gwamnatin Birtaniya Na Damuwa Kan Yadda Ake Neman A Mayar Da Kayayyakin Tarihi Da Ta Mallaka

December 4, 2023
Babban Edita Dan Kasar Ghana: A Bayyana Yadda Sin Da Afirka Suke Hadin Gwiwa Da Juna

Babban Edita Dan Kasar Ghana: A Bayyana Yadda Sin Da Afirka Suke Hadin Gwiwa Da Juna

December 4, 2023
Sojojin Nijeriya Sun Dauki Alhakin Kai Harin Bam Cikin Kuskure A Wurin Taron Mauludi A Kaduna

Sojojin Nijeriya Sun Dauki Alhakin Kai Harin Bam Cikin Kuskure A Wurin Taron Mauludi A Kaduna

December 4, 2023
Jami’ar EDF: Matakan Lardin Guangdong Na Sin Kan Magance Sauyin Yanayi Abin Koyi Ne

Jami’ar EDF: Matakan Lardin Guangdong Na Sin Kan Magance Sauyin Yanayi Abin Koyi Ne

December 4, 2023
Yadda Likitocin Nijeriya 1,616 Suka Koma Aiki Zuwa Kasar Birtaniya 

Yadda Likitocin Nijeriya 1,616 Suka Koma Aiki Zuwa Kasar Birtaniya 

December 4, 2023
Xi Jinping Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron Kasa Da Kasa Na Congdu Na 2023

Xi Jinping Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron Kasa Da Kasa Na Congdu Na 2023

December 4, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.