ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Shugabannin Kasa Da Kasa Da Manyan ‘Yan Kasuwa Suka Yi Ta Kawo Ziyara Kasar Sin?

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

Daga ranar 18 zuwa 21 ga wata, shugaban kasar Gabon Ali Bango Ondimba ya kawo ziyarar aiki kasar Sin bisa gayyatar da aka yi masa, inda shugabannin kasashen biyu suka tsai da kudurin daga matsayin cikakkiyar dangantakar hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu, zuwa cikakkiyar dangantakar abokantaka ta hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare.

Shugaba Ali Bango ya kasance shugaba na farko daga nahiyar Afirka da kasar Sin ta karba a wannan shekara, haka kuma, yana daga cikin shugabannin kasashe da shiyyoyi da suka kawo ziyara kasar Sin cikin lokacin da bai kai wata daya ba, wato biyowa bayan ziyarar firaministocin Spaniya, da Malaysia da Singapore, da shugaban kasar Faransa, da shugabar tarayyar Turai, sai kuma shugaban kasar Brazil.

  • An Bude Bikin Fina-finai Na Kasa Da Kasa Na Beijing Karo Na 13

Ban da su kuma, kusan manyan jagororin kamfanonin kasa da kasa guda 100 da suka hada da Apple, da Mercedes-Benz, da makamantansu ma suka ziyarci kasar Sin, don neman damammaki na kasuwanci.

ADVERTISEMENT

Amma me ya sa shugabannin kasa da kasa da manyan ‘yan kasuwa suka yi ta kawo ziyara kasar Sin? A yanayin da ake ciki na rashin samun kwanciyar hankali da kuma rashin tabbas, me ya sa kasashen duniya suka rika zura ido ga kasar Sin?
Domin amsa tambayoyin, za mu fara da yin nazari kan yanayin siyasar da ake ciki a duniya, inda yanzu haka ake fuskantar tashin hankali da sauye-sauye, inda kasashen yamma da ke karkashin jagorancin Amurka suka yi ta haifar da rarrabuwar kawuna, da yin fito-na-fito a tsakanin kasashen duniya, matakin da ya jawo damuwa da rashin jin dadi ga kasashe da dama. Kasar Sin a nata bangaren, tana ganin duniya ta ishi dukkanin kasashe su bunkasa kan su, kuma ta ba da shawarar kafa sabon salon dangantakar kasa da kasa mai girmama juna, da adalci, da hadin gwiwar cin moriyar juna, inda bi da bi, ta gabatar da manufar gina zaman al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya, da shawarar ziri daya da hanya daya, da shawarar raya duniya, da shawarar kiyaye tsaron duniya, da kuma shawarar wayin kai ta duniya, wadanda suke kunshe da tunanin gargajiya na kasar na rungumar zaman lafiya da kiyaye bambancin juna, wadanda kuma suka samu karbuwa daga akasarin kasashen duniya.

Shugaban kasar Gabon kafin ya fara wannan ziyara ma ya yaba da wadannan shawarwari da kasar Sin ya gabatar, yana mai cewa, shawarwarin za su taimaka ga kiyaye zaman lafiya da tsaro a duniya, tare da tabbatar da ci gaban kasa da kasa. Shi ma shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron a yayin ziyarar sa ya ce, Faransa na nacewa ga manufar diflomasiyya mai ‘yanci, kuma tana ganin ya kamata Turai ta kiyaye ‘yancinta ta fannin tsare-tsarenta, har wa yau ya bayyana rashin amincewa da jawo rarrabuwar kawuna, da yin fito-na-fito a tsakanin kasa da kasa.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

A fannin tattalin arzikinta kuma, tun bayan da kasar Sin ta inganta matakan kandagarkin annobar Covid-19, tattalin arzikin kasar Sin ya farfado. Alkaluman da hukumar kididdiga ta kasar Sin ta samar da kwanan nan sun shaida cewa, a farkon watannin ukun bana, mizanin tattalin arziki na GDP na kasar ya kai yuan trilliyan 28499.7, wanda ya karu da kaso 4.5% bisa na makamancin lokacin bara, har ma hukumomin kasa da kasa da dama sun kyautata hasashensu kan bunkasuwar tattalin arzikin kasar cikin wannan shekara.

Kasancewarta kasa mafin karfin tattalin arziki na biyu a duniya, farfadowar tattalin arzikin kasar na amfanar duniya baki daya a maimakon ita kanta. Babbar darektar asusun ba da lamuni na duniya IMF, Kristalina Georgieva ta ce, farfadowar tattalin arzikin kasar Sin na nufin kasar Sin ka iya bayar da gudummawar da za ta kai kaso 1/3, ko ma fiye da haka ga ci gaban tattalin arzikin duniya a bana. Abu mafi muhimmanci kuma shi ne yadda kasar Sin ke nacewa ga kiyaye dunkulewar ci gaban duniya, da ma inganta bude kofarta ga ketare, ta yadda karin kasashen duniya za su ci gajiyar bunkasuwarta.

Daidai da yadda Ola Källenius, shugaban darektocin kamfanin Mercedes-Benz, wanda ya kawo ziyara kasar Sin kwanan baya ya fada, cewa “za mu ci gaba da zuba jari ga kasar Sin, kasancewar yadda kasar Sin na kiyaye bunkasuwarta, da bude kofarta ga ketare, ya samar da damammaki masu daraja gare mu.”

Har kullum kasar Sin na rungumar dunkulewar duniya baki daya, kuma tana fatan ganin bunkasuwar kasa da kasa ta bai daya. Ko a tabbatar da ‘yancin kai ta fannin siyasa, ko kuma a dogara ga wasu, ko a bude wa juna kofa ta fannin tattalin arziki, ko kuma a rika yin gaba da juna, duk kasa mai hankali za ta yi zabin da ya dace.(Lubabatu)

Kasar Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Baba Buhari: Madugun Cin Bashi A Jamhuriya Ta Hudu

Baba Buhari: Madugun Cin Bashi A Jamhuriya Ta Hudu

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.