• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mene Ne Dalilin Da Ya Sa Kamfanonin Waje Su Zuba Jari Ga Kasar Sin?

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Jari

An gudanar da bikin baje kolin zuba jari da cinikayya na kasa da kasa na kasar Sin karo na 24 (CIFIT) a birnin Xiamen na lardin Fujian dake kasar tun daga ranar 8 zuwa 11 ga wannan wata, kuma an kebe wani bangare na musamman na zuba jari ga kasar Sin karo na farko, da mai da hankali ga sabon karfin samar da hajoji da hidimomi masu karko, kuma ‘yan kasuwa kimanin dubu 80 daga kasashe da yankuna 120 sun halarci bikin. Bisa kididdigar da aka yi, an cimma yarjejeniyoyin hadin gwiwa 688 a yayin bikin, yawan jarin da aka shirya zubawa ya kai Yuan biliyan 488.92.

 

Bikin shi ne biki na farko da Sin ta gudanar game da batun zuba jari bayan da aka gudanar da cikakken zama na 3 na kwamitin kolin Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin JKS karo na 20, wanda ya kasance muhimmin dandalin fahimtar Sin da neman dama a Sin ga kamfanonin kasashen waje. Wakilan kamfanonin kasa da kasa sun bayyana cewa, ya kamata a rungumi damar kasuwar kasar Sin, an yawaita ambaton kalmomin “zuba jari ga kasar Sin” a yayin bikin.

 

Kasuwar kasar Sin ta kiyaye samar da dama ga duniya. An kiyaye kyautata tsarin kashe kudi, da sa kaimi ga samar da kayayyaki da hidimomi masu inganci. Haka zalika kuma kasar Sin tana da kwarewa wajen samar da kayayyaki, hakan ya ba da tabbaci ga kamfanonin kasashen waje da su zuba jari da gudanar da ayyukansu. Kana kirkire-kirkire ya zama muhimmin karfi wajen sa kaimi ga bunkasuwar tattalin arzikin kasar Sin, saboda karin kamfanonin kasashen waje sun maida kasar Sin a matsayin wurin yin kirkire-kirkire. A yayin bikin a wannan karo, an gabatar da rahoton zuba jarin Sin da kasar ta zuba a kasashen waje na shekarar 2024, an ce, kasar Sin ta kasance kasa ta biyu mafi jawo jarin waje a duniya a shekarar 2023, Sin ta ci gaba da kasancewa kasa mafi jawo jarin kasa da kasa a duniya. (Zainab Zhang)

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

November 7, 2025
Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta

November 7, 2025
Xi Jinping Ya Taya Paul Biya Murnar Tazarce a Kamaru
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Taya Paul Biya Murnar Tazarce a Kamaru

November 7, 2025
Next Post
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi

Kwangilar Biliyan 30: PDP Ta Bukaci EFCC Ta Binciki Gwamnatin Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

November 7, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya

November 7, 2025
An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

November 7, 2025
Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

November 7, 2025
Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta

Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta

November 7, 2025
Xi Jinping Ya Taya Paul Biya Murnar Tazarce a Kamaru

Xi Jinping Ya Taya Paul Biya Murnar Tazarce a Kamaru

November 7, 2025
Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026

Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026

November 7, 2025
An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano

An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano

November 7, 2025

Ma’aikatan NPA Wasu Ginshikai Ne Na Ciyar Da NPA Gaba —Dantsoho

November 7, 2025
Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.