• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mene Ne Dalilin Da Ya Sa Wakilan Amurka Suka Ce Ba Dole Ne “Tarkon Thucydides” Ya Faru Ba?

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Mene Ne Dalilin Da Ya Sa Wakilan Amurka Suka Ce Ba Dole Ne “Tarkon Thucydides” Ya Faru Ba?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi shawarwari jiya Laraba a nan birnin Beijing, da wakilan bangarorin masana’antu da kasuwanci da ilimi na Amurka, wadanda suka kawo ziyara kasar Sin, al’amarin da ya ja hankalin kasa da kasa. A cewar shugaba Xi, matsayar da aka cimma mafi girma tsakaninsa da shugaban Amurka Joe Biden a wajen shawarwarin da suka yi a San Francisco a bara shi ne, a tabbatar da bunkasar dangantakar Sin da Amurka yadda ya kamata, da kara kyautata ta. Su ma a nasu bangaren, wakilan Amurka sun ce, “tarkon Thucydides” ba dole ne ya faru ba.

“Tarkon Thucydides” na nufin, dole ne wata sabuwar kasa dake tasowa, ta kalubalanci manyan kasashe masu ci gaba, su kuma kasashen masu ci gaba, dole za su dauki matakin taka birki ga ci gaban kasar dake tasowa, ke nan rikici har ma yaki ka iya tasowa tsakaninsu. Abun sha’awa a nan shi ne, wanda ya bullo da wannan ra’ayin na “tarkon Thucydides”, kana wanda ya kafa makarantar gwamnati ta John F. Kennedy dake jami’ar Harvard, Graham Allison, na daya daga cikin wakilan Amurka da suka halarci shawarwarin. To, mene ne dalilin da ya sa wakilan Amurka suka ce ba dole ne “tarkon Thucydides” ya faru ba?

  • Zhao Leji: Zuba Jari A Sin Zuba Jari Ne Don Gaba
  • CMG Ya Kaddamar Da Wasu Sabbin Shirye-Shiryen Bidiyo Masu Amfani Da Fasahar AI

Na farko, nasarorin da Sin da Amurka suka cimma, damarmaki ne ga juna, al’amarin da aka riga aka tabbatar da shi sau da dama. Hakikanin gaskiya, daga cikin wakilan bangarorin masana’antu da kasuwanci na Amurka da suka halarci shawarwarin a wannan karo, akwai da yawa da suka ci gajiya daga hadin-gwiwar Sin da Amurka ta fannin tattalin arziki da kasuwanci.

“Tarkon Thucydides” ba dole ne ya faru ba, magana ce dake kunshe da kyakkyawan fatan mutanen bangarorin masana’antu da kasuwanci da ilimi na Amurka ga shugabannin kasarsu, wato su fahimci kasar Sin yadda ya kamata. Idan an waiwayi dangantakar Sin da Amurka a ‘yan shekarun nan, babban abu shi ne Amurka na mayar da kasar Sin a matsayin babbar aminiyar hamayyarta bisa manyan tsare-tsare.

Haka zalika, “tarkon Thucydides” ba dole ne ya faru ba, saboda mu’amala da zumuncin dake tsakanin al’ummun Sin da Amurka.

Labarai Masu Nasaba

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

A bana ne ake cika shekaru 45 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da Amurka. A halin yanzu, ana kara samun muradu iri daya tsakanin kasashen biyu. “Tarkon Thucydides” ba dole ne ya faru ba, ra’ayi ne daya da aka cimma tsakanin mutanen bangarorin masana’antu da kasuwanci da ilimi na Amurka, wanda kuma ya kamata ya kasance ra’ayi daya da aka cimma tsakanin shugabannin kasar. (Murtala Zhang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Me Ke Jawo Hankalin Kamfanonin Kasa Da Kasa Zuwa Sin?

Next Post

Me Sabon Matakin Kasar Philippines Game Da Tekun Kudancin Sin Ke Nufi?

Related

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?
Daga Birnin Sin

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

3 hours ago
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

4 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

6 hours ago
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

6 hours ago
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya
Daga Birnin Sin

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

8 hours ago
Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC
Daga Birnin Sin

Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

9 hours ago
Next Post
Me Sabon Matakin Kasar Philippines Game Da Tekun Kudancin Sin Ke Nufi?

Me Sabon Matakin Kasar Philippines Game Da Tekun Kudancin Sin Ke Nufi?

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hukumar NRC Ta Dakatar Da Zirga-zirgar Jiragen Kasa Na Abuja zuwa Kaduna

August 26, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

August 26, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

August 26, 2025
Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

August 26, 2025
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.