• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mene Ne Dalilin Da Ya Sa Wakilan Amurka Suka Ce Ba Dole Ne “Tarkon Thucydides” Ya Faru Ba?

by CGTN Hausa
2 years ago
Amurka

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi shawarwari jiya Laraba a nan birnin Beijing, da wakilan bangarorin masana’antu da kasuwanci da ilimi na Amurka, wadanda suka kawo ziyara kasar Sin, al’amarin da ya ja hankalin kasa da kasa. A cewar shugaba Xi, matsayar da aka cimma mafi girma tsakaninsa da shugaban Amurka Joe Biden a wajen shawarwarin da suka yi a San Francisco a bara shi ne, a tabbatar da bunkasar dangantakar Sin da Amurka yadda ya kamata, da kara kyautata ta. Su ma a nasu bangaren, wakilan Amurka sun ce, “tarkon Thucydides” ba dole ne ya faru ba.

“Tarkon Thucydides” na nufin, dole ne wata sabuwar kasa dake tasowa, ta kalubalanci manyan kasashe masu ci gaba, su kuma kasashen masu ci gaba, dole za su dauki matakin taka birki ga ci gaban kasar dake tasowa, ke nan rikici har ma yaki ka iya tasowa tsakaninsu. Abun sha’awa a nan shi ne, wanda ya bullo da wannan ra’ayin na “tarkon Thucydides”, kana wanda ya kafa makarantar gwamnati ta John F. Kennedy dake jami’ar Harvard, Graham Allison, na daya daga cikin wakilan Amurka da suka halarci shawarwarin. To, mene ne dalilin da ya sa wakilan Amurka suka ce ba dole ne “tarkon Thucydides” ya faru ba?

  • Zhao Leji: Zuba Jari A Sin Zuba Jari Ne Don Gaba
  • CMG Ya Kaddamar Da Wasu Sabbin Shirye-Shiryen Bidiyo Masu Amfani Da Fasahar AI

Na farko, nasarorin da Sin da Amurka suka cimma, damarmaki ne ga juna, al’amarin da aka riga aka tabbatar da shi sau da dama. Hakikanin gaskiya, daga cikin wakilan bangarorin masana’antu da kasuwanci na Amurka da suka halarci shawarwarin a wannan karo, akwai da yawa da suka ci gajiya daga hadin-gwiwar Sin da Amurka ta fannin tattalin arziki da kasuwanci.

“Tarkon Thucydides” ba dole ne ya faru ba, magana ce dake kunshe da kyakkyawan fatan mutanen bangarorin masana’antu da kasuwanci da ilimi na Amurka ga shugabannin kasarsu, wato su fahimci kasar Sin yadda ya kamata. Idan an waiwayi dangantakar Sin da Amurka a ‘yan shekarun nan, babban abu shi ne Amurka na mayar da kasar Sin a matsayin babbar aminiyar hamayyarta bisa manyan tsare-tsare.

Haka zalika, “tarkon Thucydides” ba dole ne ya faru ba, saboda mu’amala da zumuncin dake tsakanin al’ummun Sin da Amurka.

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

A bana ne ake cika shekaru 45 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da Amurka. A halin yanzu, ana kara samun muradu iri daya tsakanin kasashen biyu. “Tarkon Thucydides” ba dole ne ya faru ba, ra’ayi ne daya da aka cimma tsakanin mutanen bangarorin masana’antu da kasuwanci da ilimi na Amurka, wanda kuma ya kamata ya kasance ra’ayi daya da aka cimma tsakanin shugabannin kasar. (Murtala Zhang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona
Daga Birnin Sin

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Next Post
Me Sabon Matakin Kasar Philippines Game Da Tekun Kudancin Sin Ke Nufi?

Me Sabon Matakin Kasar Philippines Game Da Tekun Kudancin Sin Ke Nufi?

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II

October 29, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.