ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mene Ne Dalilin Da Ya Sa Wakilan Amurka Suka Ce Ba Dole Ne “Tarkon Thucydides” Ya Faru Ba?

by CGTN Hausa
2 years ago
Amurka

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi shawarwari jiya Laraba a nan birnin Beijing, da wakilan bangarorin masana’antu da kasuwanci da ilimi na Amurka, wadanda suka kawo ziyara kasar Sin, al’amarin da ya ja hankalin kasa da kasa. A cewar shugaba Xi, matsayar da aka cimma mafi girma tsakaninsa da shugaban Amurka Joe Biden a wajen shawarwarin da suka yi a San Francisco a bara shi ne, a tabbatar da bunkasar dangantakar Sin da Amurka yadda ya kamata, da kara kyautata ta. Su ma a nasu bangaren, wakilan Amurka sun ce, “tarkon Thucydides” ba dole ne ya faru ba.

“Tarkon Thucydides” na nufin, dole ne wata sabuwar kasa dake tasowa, ta kalubalanci manyan kasashe masu ci gaba, su kuma kasashen masu ci gaba, dole za su dauki matakin taka birki ga ci gaban kasar dake tasowa, ke nan rikici har ma yaki ka iya tasowa tsakaninsu. Abun sha’awa a nan shi ne, wanda ya bullo da wannan ra’ayin na “tarkon Thucydides”, kana wanda ya kafa makarantar gwamnati ta John F. Kennedy dake jami’ar Harvard, Graham Allison, na daya daga cikin wakilan Amurka da suka halarci shawarwarin. To, mene ne dalilin da ya sa wakilan Amurka suka ce ba dole ne “tarkon Thucydides” ya faru ba?

  • Zhao Leji: Zuba Jari A Sin Zuba Jari Ne Don Gaba
  • CMG Ya Kaddamar Da Wasu Sabbin Shirye-Shiryen Bidiyo Masu Amfani Da Fasahar AI

Na farko, nasarorin da Sin da Amurka suka cimma, damarmaki ne ga juna, al’amarin da aka riga aka tabbatar da shi sau da dama. Hakikanin gaskiya, daga cikin wakilan bangarorin masana’antu da kasuwanci na Amurka da suka halarci shawarwarin a wannan karo, akwai da yawa da suka ci gajiya daga hadin-gwiwar Sin da Amurka ta fannin tattalin arziki da kasuwanci.

ADVERTISEMENT

“Tarkon Thucydides” ba dole ne ya faru ba, magana ce dake kunshe da kyakkyawan fatan mutanen bangarorin masana’antu da kasuwanci da ilimi na Amurka ga shugabannin kasarsu, wato su fahimci kasar Sin yadda ya kamata. Idan an waiwayi dangantakar Sin da Amurka a ‘yan shekarun nan, babban abu shi ne Amurka na mayar da kasar Sin a matsayin babbar aminiyar hamayyarta bisa manyan tsare-tsare.

Haka zalika, “tarkon Thucydides” ba dole ne ya faru ba, saboda mu’amala da zumuncin dake tsakanin al’ummun Sin da Amurka.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

A bana ne ake cika shekaru 45 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da Amurka. A halin yanzu, ana kara samun muradu iri daya tsakanin kasashen biyu. “Tarkon Thucydides” ba dole ne ya faru ba, ra’ayi ne daya da aka cimma tsakanin mutanen bangarorin masana’antu da kasuwanci da ilimi na Amurka, wanda kuma ya kamata ya kasance ra’ayi daya da aka cimma tsakanin shugabannin kasar. (Murtala Zhang)

Amurka
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Me Sabon Matakin Kasar Philippines Game Da Tekun Kudancin Sin Ke Nufi?

Me Sabon Matakin Kasar Philippines Game Da Tekun Kudancin Sin Ke Nufi?

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.