• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mene Ne Ma’anar Sakon Xi Jinping Kan Zagayowar Ranar Kafuwar JKS?

byCMG Hausa
2 years ago
JKS

Ranar 1 ga watan Yuli ne aka cika shekaru 102 da kafuwar Jam’iyyar Kwaminis ta Kasar Sin wato JKS. A daidai lokacin da ake bikin wannan rana, babban sakataren kwamitin tsakiyar JKS, shugaban kasa, kana, shugaban kwamitin soja na kasar Sin, Xi Jinping ya bukaci a warware matsalar musamman dake gaban jam’iyyar, da kyautata tsarin gudanarwar harkokin jam’iyyar daga dukkan fannoni, da kara kwarewar aikin jami’an kasar, ta yadda za su ba da gudummawa wajen farfado da al’ummar Sinawa baki daya. Mene ne ma’anar sakon da Xi Jinping ya bayar, kuma mene ne alakar mulkin jam’iyya da na kasa?

Duk wanda ya fahimci tarihin kasar Sin ya san cewa, tarihin kasar Sin cikin shekaru 100 da suka gabata, ba a iya raba shi da jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin ba, kuma tasowa ko faduwar kasar yana da alaka da jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin. A cikin shekaru 100 da suka gabata, nasarar da JKS ta samu ya dogara ne kan jagoranci mai karfi, raya kanta, da gudanar da ayyukanta yadda ya kamata.

A halin yanzu, Xi na ci gaba da jagorantar aikin yin kwaskwarima ga JKS, ya kuma tsaya tsayin daka wajen gudanar da ayyukan JKS bisa tsari, da yin kwaskwarima, domin warware matsala ta musamman dake gaban wannan babbar jam’iyya a duniya, ta yadda jam’iyyar za ta ci gaba da ba da jagoranci ga kasar Sin, a kokarin wadatar da al’ummar ta, da neman farfadowar kasar Sin, gami da shimfida zaman lafiya mai dorewa, da tabbatar da jin dadin al’umomin duniya baki daya.

Xi Jinping na mai da matukar hankali kan gudanarwar harkokin JKS, inda ya bukaci a gudanar da harkokin JKS kamar yadda aka tsara a dukkan fannoni, kuma, ya hada wannan bukata tare da aikin gina kasa mai tsarin gurguzu ta zamani a dukkan fannoni, da zurfafa aikin kwaskwarima a dukkan fannoni, da gudanar da ayyukan kasa bisa doka a dukkan fannoni, wadanda suka kasance babbar manufa da babban tsarin gudanar da harkokin kasar Sin, lamarin da ya nuna dangantakar dake tsakanin JKS da aikin zamanintar da kasa, wayewar kan kasa, farfadowar kasa. Ma’ana, bin jagorancin JKS shi ne tushen gudanar da harkokin kasa kamar yadda ake fata. (Mai Fassarawa: Maryam Yang)

 

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?
Daga Birnin Sin

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
Next Post
gaza

Kura Ta Turnike Majalisar Dattawa Kan Nadin Shugaban Marasa Rinjaye

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version