• English
  • Business News
Thursday, October 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Sadiya Ta Mika Ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinkai Ga Babban Sakatare

by Sulaiman
2 years ago
Minista sadiya

Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ta miƙa ragamar gudanar da ayyukan ma’aikatar ga Babban Sakataren ma’aikatar, Dakta Nasir Sani Gwarzo, bayan ta kammala aikin ta cikin gagarumar nasara.

Hajiya Sadiya ta riƙe ma’aikatar ne a matsayin ministar ta ta farko har tsawon shekara uku da rabi inda ta yi wa al’umma aiki tuƙuru babu gajiyawa.

  • Yanzu-yanzu: Gwamnan Neja Ya Mika Takardun Mika Gwamnati Ga Zababben Gwamna, Bago

Hajiya Sadiya ta miƙa wasu takardu ƙunshe a cikin kundaye biyu da ke bayyana ayyukan da ta yi a ma’aikatar a ranar Juma’a a Abuja, a ƙarshen Taron Duniya kan Ayyukan Agaji na Nijeriya (wayo Nigerian International Humanitarian Summit) karo na farko wanda ma’aikatar ta ɗauki nauyin shiryawa.

A jawabin da ta yi a taron, ministar ta gode wa Babban Sakataren da daraktoci da ma’aikatan ma’aikatar da na ofishin ta saboda gagarumin goyon bayan da su ka ba ta a dukkan tsawon wa’adin riƙe muƙamin ta.

Hajiya Sadiya Umar Farouq ta kuma yi kira ga ma’aikatan da su tsaya tsayin daka kan ƙoƙarin da su ke yi na ganin an cimma nasara a muradin Shugaba Muhammadu Buhari na ‘yanto ɗimbin marasa galihu daga ƙangin fatara da yunwa.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Naira Biliyan 2.5 Na Aikin Haƙo Uranium, Mai Da Iskar Gas

NUJ Reshen Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

Ta ce: “Ga ni a yanzu ina miƙa waɗannan takardun masu ƙunshe da bayanan riƙon ragamar da na yi a matsayin Ministar farko ta Ma’aikatar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa a cikin shekaru uku da rabi da su ka gabata. Na gode maku ƙwarai da gaske saboda goyon bayan da ku ka ba ni, a yau kuma na ke miƙa ragamar ga Babban Sakatare, Dakta Nasir Sani- Gwarzo”.

Da ya ke mayar da martani, Babban Sakataren ya gode wa Ministar, sannan kuma ya yi mata fatan alheri a duk inda ta sa gaba a shekaru masu zuwa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Naira Biliyan 2.5 Na Aikin Haƙo Uranium, Mai Da Iskar Gas
Manyan Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Naira Biliyan 2.5 Na Aikin Haƙo Uranium, Mai Da Iskar Gas

October 23, 2025
NUJ Reshen Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa
Labarai

NUJ Reshen Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

October 23, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

‘Yansanda Sun Cafke Wani Matashi Ɗan Shekara 15 Da Ake Zargi Da Yin Fashi Da Makami A Gombe

October 22, 2025
Next Post
An Shirya Wa Gwamna Inuwa Kasaitaccen Bikin Raye-rayen Al’adun Gargajiya Gabanin Rantsar Da Shi 

An Shirya Wa Gwamna Inuwa Kasaitaccen Bikin Raye-rayen Al'adun Gargajiya Gabanin Rantsar Da Shi 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Naira Biliyan 2.5 Na Aikin Haƙo Uranium, Mai Da Iskar Gas

Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Naira Biliyan 2.5 Na Aikin Haƙo Uranium, Mai Da Iskar Gas

October 23, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Diflomasiyyar Shugabanni Na Matukar Taka Rawar Gani Wajen Jagorantar Dangantakar Sin Da Amurka

October 22, 2025
NUJ Reshen Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

NUJ Reshen Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

October 23, 2025
Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

October 22, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Cafke Wani Matashi Ɗan Shekara 15 Da Ake Zargi Da Yin Fashi Da Makami A Gombe

October 22, 2025
Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

October 22, 2025
An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

October 22, 2025
Adadin Yawon Shakatawa Da Mutanen Sin Suka Yi A Cikin Gida Ya Zarce Biliyan 4.998 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana

Adadin Yawon Shakatawa Da Mutanen Sin Suka Yi A Cikin Gida Ya Zarce Biliyan 4.998 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana

October 22, 2025
Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina

Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina

October 22, 2025
Kasar Sin Ta Sake Farfado Da Muhimman Koguna Da Tafkuna 88 A Kokarin Inganta Muhalli

Kasar Sin Ta Sake Farfado Da Muhimman Koguna Da Tafkuna 88 A Kokarin Inganta Muhalli

October 22, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.