• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Yaɗa Labarai Ya Nemi Masu Zanen Gine-gine Su Farfaɗo Da Tarihin Ginin  Nijeriya

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Minista Yaɗa Labarai Ya Nemi Masu Zanen Gine-gine Su Farfaɗo Da Tarihin Ginin  Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi kira ga Hukumar Masu Zanen Gine-gine ta Ƙasa (National Institute of Architects) da su shiga sahun gaba wajen yin azamar farfaɗo da kyawawan fasalin gine-ginen da ke ƙara haskaka tarihin Nijeriya.

Idris ya ce irin waɗannan gine-gine masu fasalin daɗaɗɗen tarihi su ne ke nuna irin ƙasaitar kowace ƙasa.

  • Sojojin Sama Ga INEC: Ku Biya Mu Bashi Don Mu Ji Dadin Aiki Tukuru
  • Rashin Tsaro: Atiku Ya Sake Caccakar Tinubu

Mataimakin Daraktan Yaɗa Labarai na Ma’aikatar Yaɗa Labarai, Suleiman Haruna, ya faɗa a cikin wata sanarwa da sa wa hannu, cewa ministan ya bayyana hakan ne a yayin da tawaga daga hukumar ta kai masa ziyara, a ranar Alhamis.

Ya ƙara da cewa akwai buƙatar cibiyar ta himmatu wajen taskace kayayyakin tarihi musamman masu nuna ƙasaitattun gine-gine masu tarihi domin yawancin ‘yan Nijeriya ba su ma san tarihin ƙasaitattun gine-ginen da ke yankunan su ba.

Idris ya ce: “Shin ko kun san cewa ofishin Hukumar Wayar da Kan Jama’a ta Ƙasa (NOA) a yanzu haka a Abuja, ya taɓa zama ofishin tsohon Shugaban Ƙasa, marigayi Shehu Shagari?

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

“To hatta ɗakin taro na NOA ɗin ya taɓa zama Zauren Taron Majalisar Zartaswa ta Ƙasa, inda ministoci su ka riƙa yin taron su da Shugaban Ƙasa.

“Idan ka ziyarci ofishin NOA a yau ɗin nan, za ka ga ita kan ta kujerar da marigayi Shugaba Shagari ya riƙa zama a kan ta, lokacin ya na shugaban ƙasa.”

Idris yi kira ga hukumar ta ƙwararrun masu zanen gine-ginen da su ci gaba da tuntuɓa da kuma yin aiki tare da ma’aikatar sa wajen ƙoƙarin sake wayar da kan jama’a, domin ɗabbaƙa kyawawan al’adun mu.

Ya kuma yi tsinkayen cewa jama’a su ne mafi tasirin al’adu da kowace ƙasa za ta yi alfahari da su.

Ya ƙara da cewa idan jama’a su ka rasa kyawawan ɗabi’u da ƙarancin wayewar kai a matsayin su na al’umma, to duk wani ƙoƙarin da ake son a cimma, ba zai yi nasara ba.

Ministan ya yi ƙorafi dangane da munanan ɗabi’un wasu marasa kishi, waɗanda ba su darajta gine-ginen tarihin ƙasa da sauran ababen da ke haskaka kyakkyawan tarihin mu a matsayin ƙasa, musamman Tutar Nijeriya, Tambarin Nijeriya, fasfo na shaidar ɗan ƙasa da sauran su.

Haka kuma ya ce Shugaba Bola Tinubu ya ɗau himmar kawo kyakkyawan sauyi a zukatan jama’a, dalili kenan ma ya bayar da fifiko da maida hankali kan Shirin Wayar da Kai a matsayin sabon aiki wurjanjan da ya ɗora wa Ma’aikatar Yaɗa Labarai.

Ita kuwa Shugabar Hukumar Masu Zanen Gine-gine ta Ƙasa, Mobolaji Adeniyi, ta nuna cewa a shirye hukumar take wajen haɗa kai da haɗa ƙarfi da Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai domin samun nasara wajen wayar da kan jama’a, musamman a ɓangaren kamfen don nuna wa mutane illolin da ke haddasa rugujewar gine-gine, haɗarin da ke tattare da gini maras inganci ko kayan gini marasa nagarta da sauran hanyoyin da za a taskace gine-gine masu tarihi a ƙasar nan, musamman a Babban Birnin Tarayya, Abuja.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Al’adun GargajiyaMinistan yada labaraiTarihin Ginin Nijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

CMG Ya Shirya Shagali Gabanin Liyafar Bikin Bazara A Geneva

Next Post

Kuri’ar Jin Ra’ayi Ta CGTN: Fiye Da 90% Na Masu Amfani Da Yanar Gizo Sun Yi Suka Ga ‘Yan Siyasar Amurka Kan Girman Kai Da Jahilci

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

38 minutes ago
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

1 hour ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

3 hours ago
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

5 hours ago
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

6 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

7 hours ago
Next Post
Kuri’ar Jin Ra’ayi Ta CGTN: Fiye Da 90% Na Masu Amfani Da Yanar Gizo Sun Yi Suka Ga ‘Yan Siyasar Amurka Kan Girman Kai Da Jahilci

Kuri’ar Jin Ra’ayi Ta CGTN: Fiye Da 90% Na Masu Amfani Da Yanar Gizo Sun Yi Suka Ga ‘Yan Siyasar Amurka Kan Girman Kai Da Jahilci

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.