• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Yaɗa Labarai Ya Nemi Masu Zanen Gine-gine Su Farfaɗo Da Tarihin Ginin  Nijeriya

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Minista Yaɗa Labarai Ya Nemi Masu Zanen Gine-gine Su Farfaɗo Da Tarihin Ginin  Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi kira ga Hukumar Masu Zanen Gine-gine ta Ƙasa (National Institute of Architects) da su shiga sahun gaba wajen yin azamar farfaɗo da kyawawan fasalin gine-ginen da ke ƙara haskaka tarihin Nijeriya.

Idris ya ce irin waɗannan gine-gine masu fasalin daɗaɗɗen tarihi su ne ke nuna irin ƙasaitar kowace ƙasa.

  • Sojojin Sama Ga INEC: Ku Biya Mu Bashi Don Mu Ji Dadin Aiki Tukuru
  • Rashin Tsaro: Atiku Ya Sake Caccakar Tinubu

Mataimakin Daraktan Yaɗa Labarai na Ma’aikatar Yaɗa Labarai, Suleiman Haruna, ya faɗa a cikin wata sanarwa da sa wa hannu, cewa ministan ya bayyana hakan ne a yayin da tawaga daga hukumar ta kai masa ziyara, a ranar Alhamis.

Ya ƙara da cewa akwai buƙatar cibiyar ta himmatu wajen taskace kayayyakin tarihi musamman masu nuna ƙasaitattun gine-gine masu tarihi domin yawancin ‘yan Nijeriya ba su ma san tarihin ƙasaitattun gine-ginen da ke yankunan su ba.

Idris ya ce: “Shin ko kun san cewa ofishin Hukumar Wayar da Kan Jama’a ta Ƙasa (NOA) a yanzu haka a Abuja, ya taɓa zama ofishin tsohon Shugaban Ƙasa, marigayi Shehu Shagari?

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

“To hatta ɗakin taro na NOA ɗin ya taɓa zama Zauren Taron Majalisar Zartaswa ta Ƙasa, inda ministoci su ka riƙa yin taron su da Shugaban Ƙasa.

“Idan ka ziyarci ofishin NOA a yau ɗin nan, za ka ga ita kan ta kujerar da marigayi Shugaba Shagari ya riƙa zama a kan ta, lokacin ya na shugaban ƙasa.”

Idris yi kira ga hukumar ta ƙwararrun masu zanen gine-ginen da su ci gaba da tuntuɓa da kuma yin aiki tare da ma’aikatar sa wajen ƙoƙarin sake wayar da kan jama’a, domin ɗabbaƙa kyawawan al’adun mu.

Ya kuma yi tsinkayen cewa jama’a su ne mafi tasirin al’adu da kowace ƙasa za ta yi alfahari da su.

Ya ƙara da cewa idan jama’a su ka rasa kyawawan ɗabi’u da ƙarancin wayewar kai a matsayin su na al’umma, to duk wani ƙoƙarin da ake son a cimma, ba zai yi nasara ba.

Ministan ya yi ƙorafi dangane da munanan ɗabi’un wasu marasa kishi, waɗanda ba su darajta gine-ginen tarihin ƙasa da sauran ababen da ke haskaka kyakkyawan tarihin mu a matsayin ƙasa, musamman Tutar Nijeriya, Tambarin Nijeriya, fasfo na shaidar ɗan ƙasa da sauran su.

Haka kuma ya ce Shugaba Bola Tinubu ya ɗau himmar kawo kyakkyawan sauyi a zukatan jama’a, dalili kenan ma ya bayar da fifiko da maida hankali kan Shirin Wayar da Kai a matsayin sabon aiki wurjanjan da ya ɗora wa Ma’aikatar Yaɗa Labarai.

Ita kuwa Shugabar Hukumar Masu Zanen Gine-gine ta Ƙasa, Mobolaji Adeniyi, ta nuna cewa a shirye hukumar take wajen haɗa kai da haɗa ƙarfi da Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai domin samun nasara wajen wayar da kan jama’a, musamman a ɓangaren kamfen don nuna wa mutane illolin da ke haddasa rugujewar gine-gine, haɗarin da ke tattare da gini maras inganci ko kayan gini marasa nagarta da sauran hanyoyin da za a taskace gine-gine masu tarihi a ƙasar nan, musamman a Babban Birnin Tarayya, Abuja.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Al’adun GargajiyaMinistan yada labaraiTarihin Ginin Nijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

CMG Ya Shirya Shagali Gabanin Liyafar Bikin Bazara A Geneva

Next Post

Kuri’ar Jin Ra’ayi Ta CGTN: Fiye Da 90% Na Masu Amfani Da Yanar Gizo Sun Yi Suka Ga ‘Yan Siyasar Amurka Kan Girman Kai Da Jahilci

Related

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

9 hours ago
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta
Labarai

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

11 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

14 hours ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

15 hours ago
‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki
Labarai

‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki

16 hours ago
Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

17 hours ago
Next Post
Kuri’ar Jin Ra’ayi Ta CGTN: Fiye Da 90% Na Masu Amfani Da Yanar Gizo Sun Yi Suka Ga ‘Yan Siyasar Amurka Kan Girman Kai Da Jahilci

Kuri’ar Jin Ra’ayi Ta CGTN: Fiye Da 90% Na Masu Amfani Da Yanar Gizo Sun Yi Suka Ga ‘Yan Siyasar Amurka Kan Girman Kai Da Jahilci

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

July 26, 2025
Minista

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

July 26, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.