ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Yaɗa Labarai Ya Nemi Masu Zanen Gine-gine Su Farfaɗo Da Tarihin Ginin  Nijeriya

by Sulaiman
2 years ago
Minista

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi kira ga Hukumar Masu Zanen Gine-gine ta Ƙasa (National Institute of Architects) da su shiga sahun gaba wajen yin azamar farfaɗo da kyawawan fasalin gine-ginen da ke ƙara haskaka tarihin Nijeriya.

Idris ya ce irin waɗannan gine-gine masu fasalin daɗaɗɗen tarihi su ne ke nuna irin ƙasaitar kowace ƙasa.

  • Sojojin Sama Ga INEC: Ku Biya Mu Bashi Don Mu Ji Dadin Aiki Tukuru
  • Rashin Tsaro: Atiku Ya Sake Caccakar Tinubu

Mataimakin Daraktan Yaɗa Labarai na Ma’aikatar Yaɗa Labarai, Suleiman Haruna, ya faɗa a cikin wata sanarwa da sa wa hannu, cewa ministan ya bayyana hakan ne a yayin da tawaga daga hukumar ta kai masa ziyara, a ranar Alhamis.

ADVERTISEMENT

Ya ƙara da cewa akwai buƙatar cibiyar ta himmatu wajen taskace kayayyakin tarihi musamman masu nuna ƙasaitattun gine-gine masu tarihi domin yawancin ‘yan Nijeriya ba su ma san tarihin ƙasaitattun gine-ginen da ke yankunan su ba.

Idris ya ce: “Shin ko kun san cewa ofishin Hukumar Wayar da Kan Jama’a ta Ƙasa (NOA) a yanzu haka a Abuja, ya taɓa zama ofishin tsohon Shugaban Ƙasa, marigayi Shehu Shagari?

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

“To hatta ɗakin taro na NOA ɗin ya taɓa zama Zauren Taron Majalisar Zartaswa ta Ƙasa, inda ministoci su ka riƙa yin taron su da Shugaban Ƙasa.

“Idan ka ziyarci ofishin NOA a yau ɗin nan, za ka ga ita kan ta kujerar da marigayi Shugaba Shagari ya riƙa zama a kan ta, lokacin ya na shugaban ƙasa.”

Idris yi kira ga hukumar ta ƙwararrun masu zanen gine-ginen da su ci gaba da tuntuɓa da kuma yin aiki tare da ma’aikatar sa wajen ƙoƙarin sake wayar da kan jama’a, domin ɗabbaƙa kyawawan al’adun mu.

Ya kuma yi tsinkayen cewa jama’a su ne mafi tasirin al’adu da kowace ƙasa za ta yi alfahari da su.

Ya ƙara da cewa idan jama’a su ka rasa kyawawan ɗabi’u da ƙarancin wayewar kai a matsayin su na al’umma, to duk wani ƙoƙarin da ake son a cimma, ba zai yi nasara ba.

Ministan ya yi ƙorafi dangane da munanan ɗabi’un wasu marasa kishi, waɗanda ba su darajta gine-ginen tarihin ƙasa da sauran ababen da ke haskaka kyakkyawan tarihin mu a matsayin ƙasa, musamman Tutar Nijeriya, Tambarin Nijeriya, fasfo na shaidar ɗan ƙasa da sauran su.

Haka kuma ya ce Shugaba Bola Tinubu ya ɗau himmar kawo kyakkyawan sauyi a zukatan jama’a, dalili kenan ma ya bayar da fifiko da maida hankali kan Shirin Wayar da Kai a matsayin sabon aiki wurjanjan da ya ɗora wa Ma’aikatar Yaɗa Labarai.

Ita kuwa Shugabar Hukumar Masu Zanen Gine-gine ta Ƙasa, Mobolaji Adeniyi, ta nuna cewa a shirye hukumar take wajen haɗa kai da haɗa ƙarfi da Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai domin samun nasara wajen wayar da kan jama’a, musamman a ɓangaren kamfen don nuna wa mutane illolin da ke haddasa rugujewar gine-gine, haɗarin da ke tattare da gini maras inganci ko kayan gini marasa nagarta da sauran hanyoyin da za a taskace gine-gine masu tarihi a ƙasar nan, musamman a Babban Birnin Tarayya, Abuja.

Minista
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
Next Post
Kuri’ar Jin Ra’ayi Ta CGTN: Fiye Da 90% Na Masu Amfani Da Yanar Gizo Sun Yi Suka Ga ‘Yan Siyasar Amurka Kan Girman Kai Da Jahilci

Kuri’ar Jin Ra’ayi Ta CGTN: Fiye Da 90% Na Masu Amfani Da Yanar Gizo Sun Yi Suka Ga ‘Yan Siyasar Amurka Kan Girman Kai Da Jahilci

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.