• English
  • Business News
Saturday, May 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Ƙaryata Jita-jitar Mayar Da Taron Bayanin Ministoci Zuwa London

by Sulaiman
9 hours ago
in Labarai
0
Minista Ya Ƙaryata Jita-jitar Mayar Da Taron Bayanin Ministoci Zuwa London
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya musanta rahotannin da ke yawo cewa wai an mayar da Jerin Taron Bayanin Ministoci Ga ‘Yan Jarida daga Abuja zuwa London.

 

Ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabi a lokacin buɗe jerin taron na takwas da aka gudanar a Cibiyar ‘Yan Jarida ta Ƙasa da ke Abuja.

  • Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232
  • Rashin Tsaro Da Raba Wa Manoma Kayan Aiki Kan Lokaci Na Baraza Ga Wadata Kasa Da Abinci

Ya ce: “Ga amsar ku ga ji-ta-ji-tar cewa wai za a mayar da taron ‘yan jarida zuwa ƙetare. Muna da nauyin da ya rataya a wuyan mu na farko ga Nijeriya, shi ya sa muke gayyatar ministoci su zo nan su yi wa ‘yan Nijeriya da ma waɗanda ke waje jawabi kai-tsaye daga nan Cibiyar ‘Yan Jarida ta Ƙasa da ke Abuja.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara

Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Farfaɗo Da Sashin Raba Wutar Lantarki A Nijeriya

“Don haka, idan kuna tunanin cewa taron bayanin ministoci, kamar yadda wasu ke yaɗa cewa za a mayar da shi zuwa wajen ƙasar, ba gaskiya ba ne.

 

“Wannan dandamali da Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai take samarwa, nan ne inda abin ke faruwa, a nan ƙasar.”

 

Taron ya samu halartar Ministar Harkokin Al’adu da Tattalin Arzikin Ƙirƙira, Hannatu Musawa; da Ministan Ruwa da Tsaftace Muhalli, Farfesa Joseph Utsev, da kuma Ministan Ayyuka, Sanata David Umahi.

 

Sanata Umahi, wanda aka ruwaito ba daidai ba cewa yana daga cikin ministocin da za su gabatar da nasarorin Gwamnatin Shugaban Ƙasa Tinubu a wani taro a London, ya goyi bayan furucin Idris, yana mai cewa rahoton ba gaskiya ba ne.

 

Idris ya kuma taɓo batun tattalin arzikin ƙasa, inda ya yi nuni da Rahoton Nuna Canjin Farashin Kayayyaki (CPI) na watan Afrilu 2025 da Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa ta fitar.

 

Ya ce: “Yau, ina farin cikin bayyana wani labari mai daɗi daga Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa, wadda ta fitar da Rahoton Nuna Canjin Farashin Kayayyaki (CPI) na watan Afrilu 2025, jiya. Bisa ga rahoton, adadin hauhawar farashin kayayyaki na watan Afrilu ya tsaya a kashi 23.71, wanda ke nuna ragin kashi 0.52 daga 24.23 da aka rubuta a watan Maris 2025.

 

“Haka kuma, idan aka kwatanta wata da wata, hauhawar farashin ya ragu sosai da kashi 2.04, daga 3.90 a Maris zuwa 1.86 a Afrilu.

 

“Wannan ba ya faruwa haka ziƙau. Tsare-tsaren Shugaban Ƙasa da aka mayar da hankali a kai su ne suke haifar da ɗa mai ido. Fa’idar gyare-gyaren da ake yi, ko da yake a hankali suke zuwa, tabbatattu ne kuma mutum zai iya auna su.”

 

Ya bayyana cewa hauhawar farashin kayayyakin abinci – wanda ke ɗaya daga cikin manyan abubuwan da ke haddasa hauhawar farashi – ya fara raguwa sakamakon tsare-tsaren Shugaban Ƙasa Tinubu.

 

Ya ce: “Ɗaya daga cikin manyan alamu na sauƙin da ake samu shi ne ƙimar hauhawar farashin abinci. Duk da cewa farashin abinci har yanzu yana damun mutane da dama a Nijeriya, hauhawar farashin abinci daga shekara zuwa shekara ya ragu zuwa kashi 21.26 a watan Afrilu.

 

“Idan aka duba wata zuwa wata kuwa, ya ragu zuwa kashi 2.06, daga kashi 2.18 da aka samu a Maris. Wannan cigaba mai kyau ya samo asali ne daga ragin farashin muhimman kayan abinci irin su garin masara, hatsi, garin doya, kuɓewa, gyaɗa, shinkafa, da wake.

 

“Jama’a, mun san cewa har yanzu ba mu kai inda muke fatar kaiwa ba. Amma waɗannan alƙaluman da aka samu kwanan nan suna ba mu cikakken dalili na yin fatan alheri. Suna nuna cewa matakan da muka ɗauka masu wahala sun fara haifar da kyakkyawan sakamako. Kuma yayin da farashi yake sauka, muna sa ran ganin sauƙi a ƙarfin sayen kayan masarufi da kuma rayuwar jama’a gaba ɗaya.”

 

Ministan ya tabbatar wa da ‘yan Nijeriya cewa Gwamnatin Tinubu za ta ci gaba da ɗaukar matakan da ke mayar da hankali kan rayuwar jama’a don kawo sauƙi, da dawo da daidaiton tattalin arziki, da inganta walwala ga kowa da kowa.

 

Ya kuma roƙi kafafen yaɗa labarai da su ci gaba da ba da labarin irin wannan cigaban cikin gaskiya, yana mai jaddada cewa gwamnati za ta ci gaba da zama mai gabatar da komai a bayyane kuma amintacciya ga ‘yan ƙasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

GORON JUMA’A 16/05/2025

Next Post

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 2, Sun Kwato Shanu 1,000 A Taraba

Related

Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara
Labarai

Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara

2 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Farfaɗo Da Sashin Raba Wutar Lantarki A Nijeriya
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Farfaɗo Da Sashin Raba Wutar Lantarki A Nijeriya

5 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2, Sun Ƙwato Shanun Sata 1,000 A Taraba
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2, Sun Ƙwato Shanun Sata 1,000 A Taraba

6 hours ago
Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 2, Sun Kwato Shanu 1,000 A Taraba
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 2, Sun Kwato Shanu 1,000 A Taraba

8 hours ago
Zargin Cin Zarafi: Gaskiyar Halin Da Ake Ciki A Gidan Yarin Goron Dutse
Labarai

Zargin Cin Zarafi: Gaskiyar Halin Da Ake Ciki A Gidan Yarin Goron Dutse

11 hours ago
Nijeriya Na Bukatar Dala Biliyan 10 Kowace Shekara Domin Samun Ingantacciyar Wutar Lantarki — Minista
Labarai

Nijeriya Na Bukatar Dala Biliyan 10 Kowace Shekara Domin Samun Ingantacciyar Wutar Lantarki — Minista

12 hours ago
Next Post
Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 2, Sun Kwato Shanu 1,000 A Taraba

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 2, Sun Kwato Shanu 1,000 A Taraba

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara

Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara

May 16, 2025
Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal

Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal

May 16, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

May 16, 2025
JAMB Ta Ƙaddamar Da Binciken Gaggawa Kan Sakamakon Jarrabawar Bana Bayan Jerin Ƙorafe-Ƙorafe 

JAMB Ta Ƙaddamar Da Binciken Gaggawa Kan Sakamakon Jarrabawar Bana Bayan Jerin Ƙorafe-Ƙorafe 

May 16, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Farfaɗo Da Sashin Raba Wutar Lantarki A Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Farfaɗo Da Sashin Raba Wutar Lantarki A Nijeriya

May 16, 2025
CMG Ya Gabatar Da Fasahar Tsara Shirye-Shiryen Bidiyo Da Rediyo Bisa Fasahar Sadarwa Ta 5G A ITU

CMG Ya Gabatar Da Fasahar Tsara Shirye-Shiryen Bidiyo Da Rediyo Bisa Fasahar Sadarwa Ta 5G A ITU

May 16, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2, Sun Ƙwato Shanun Sata 1,000 A Taraba

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2, Sun Ƙwato Shanun Sata 1,000 A Taraba

May 16, 2025
Xi Jinping Ya Jaddada Wajibcin Koyi Da Nagartattun Halayen Wasu Mutane Masu Bukata Ta Musamman

Xi Jinping Ya Jaddada Wajibcin Koyi Da Nagartattun Halayen Wasu Mutane Masu Bukata Ta Musamman

May 16, 2025
Kasar Sin Ta Cimma Burinta A Fannin Kulla Yarjejeniyoyin Fasaha Kafin Lokacin Da Ta Tsara

Kasar Sin Ta Cimma Burinta A Fannin Kulla Yarjejeniyoyin Fasaha Kafin Lokacin Da Ta Tsara

May 16, 2025
Firaministan Sin: Tattalin Arzikin Sin Na Habaka Yadda Ya Kamata Yayin Da Kasar Ke Samun Ci Gaba

Firaministan Sin: Tattalin Arzikin Sin Na Habaka Yadda Ya Kamata Yayin Da Kasar Ke Samun Ci Gaba

May 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.