ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

JAMB Ta Ƙaddamar Da Binciken Gaggawa Kan Sakamakon Jarrabawar Bana Bayan Jerin Ƙorafe-Ƙorafe 

by Khalid Idris Doya
1 year ago
JAMB

Hukumar kula da shirya jarabawar shiga manyan makarantu (JAMB) ta kaddamar da wani bita cikin gaggawa kan tsarin Jarrabawar Shiga Manyan Makarantu (UTME) na shekarar 2025, biyo bayan korafe-korafe da dalibai da iyaye ke yi a fadin kasar na tare da zargin rashin bin ka’ida da kuma sabani a sakamakon jarabawar.

Matakin na zuwa ne kwanaki kalilan da hukumar ta sake sakamakon jarabawar bana, inda hukumar ta tabbatar da cewa ta samu jerin korafe-korafe da daman gaske. Dubban dalibai ne dai suka yi fatali da kin amincewa da sakamakon da suka samu a jarabawar, lamarin da ke janyo kokonto da shakku kan ingancin tsarin da ake bi.

  • JAMB Ta Dakatar Da Wasu Jami’anta Saboda Tilastawa Wata Daliba Cire Hijabi
  • Gwamnatin Kano Ta Soke Tsaftar Muhalli A Watan Afrilu Saboda Jarabawar JAMB

Dalibai da dama sun shiga shafukan sada zumunta, suna zargin hukumar JAMB da gazawa ta bangaren samun tangardar na’ura da suka yi imanin cewa ya yi illa ga kwazonsu da kokarinsu a yayin jarabawar.

ADVERTISEMENT

Da yake magana a Abuja, mai magana da yawun hukumar JAMB, Dakta Fabian Benjamin ya tabbatar da cewa hukumar tana duba na’urorinta a kai a kai gabanin ma gudanar da jarabawar.

“Muna hanzarta sake duba jarabawarmu na yau da kullun, wanda zai bincika kowane bangare na tsarin UTME, tun daga rajista zuwa jarrabawa da fitar da sakamako,” in ji Benjamin.

LABARAI MASU NASABA

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

Ya yi nuni da cewa hukumar tana aiki ne tare da hadin gwiwar abokan huldar waje, da suka hada da kungiyar kwararrun na’urar kwamfuta ta Nijeriya, da manyan masu jarrabawa daga manyan makarantu, da kungiyar ilimi da cibiyar bincike a Afirka. Wadannan hadin gwiwar, in ji shi, suna da nufin samar da ingantaccen bincike da kuma sahihin bincike.

“Idan an gano cewa an samu tangarda a na’ura, to za a dauki matakan gyarawa ba tare da bata wani lokaci ba,” Benjamin ya tabbatar.

Duk da wannan tabbacin da aka bayar, sama da dalibai 8,000 ne suka shigar da korafinsu a hukumance suna cewa an samu matsaloli na na’ura sosai a yayin jarabawa. Abubuwan da aka ruwaito sun hada da daskararrun allon kwamfuta, jinkirin shiga cikin tsarin zana jarabawar daga ita kwanfutar, da karewar zaman jarrabawa ba zato ba tsammani.

Binciken farko na sakamakon UTME na 2025 ya nuna cewa sama da kashi 78 na sama da dalibai miliyan 1.9 sun samu maki kasa da 200 cikin matsakaicin maki 400. Alkaluman sun kara zurfafa shakku na gazawar fasaha ko na tsari.

Benjamin ya ce duk da haka, lamarin ya tsaya kan sakamakon kamar yadda aka fitar a halin yanzu, yana mai bayyana cewa sun yi daidai da hakikanin kwazon da dalibai suka nuna. Har ila yau, ya amince da alhakin hukumar ta binciki duk rahotannin da suka dace na abubuwan da suka faru.

Sai dai hukumar ta nemi a kwantar da hankali har zuwa lokacin da za ta kammala binciko shin an samu matsala a tsarin jarabawar ko kuma gazawar kwazon ɗalibai ne.

JAMB
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
Ilimi

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

June 20, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund
Ilimi

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.