ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

JAMB Ta Ƙaddamar Da Binciken Gaggawa Kan Sakamakon Jarrabawar Bana Bayan Jerin Ƙorafe-Ƙorafe 

by Khalid Idris Doya
1 year ago
JAMB

Hukumar kula da shirya jarabawar shiga manyan makarantu (JAMB) ta kaddamar da wani bita cikin gaggawa kan tsarin Jarrabawar Shiga Manyan Makarantu (UTME) na shekarar 2025, biyo bayan korafe-korafe da dalibai da iyaye ke yi a fadin kasar na tare da zargin rashin bin ka’ida da kuma sabani a sakamakon jarabawar.

Matakin na zuwa ne kwanaki kalilan da hukumar ta sake sakamakon jarabawar bana, inda hukumar ta tabbatar da cewa ta samu jerin korafe-korafe da daman gaske. Dubban dalibai ne dai suka yi fatali da kin amincewa da sakamakon da suka samu a jarabawar, lamarin da ke janyo kokonto da shakku kan ingancin tsarin da ake bi.

  • JAMB Ta Dakatar Da Wasu Jami’anta Saboda Tilastawa Wata Daliba Cire Hijabi
  • Gwamnatin Kano Ta Soke Tsaftar Muhalli A Watan Afrilu Saboda Jarabawar JAMB

Dalibai da dama sun shiga shafukan sada zumunta, suna zargin hukumar JAMB da gazawa ta bangaren samun tangardar na’ura da suka yi imanin cewa ya yi illa ga kwazonsu da kokarinsu a yayin jarabawar.

ADVERTISEMENT

Da yake magana a Abuja, mai magana da yawun hukumar JAMB, Dakta Fabian Benjamin ya tabbatar da cewa hukumar tana duba na’urorinta a kai a kai gabanin ma gudanar da jarabawar.

“Muna hanzarta sake duba jarabawarmu na yau da kullun, wanda zai bincika kowane bangare na tsarin UTME, tun daga rajista zuwa jarrabawa da fitar da sakamako,” in ji Benjamin.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

Ya yi nuni da cewa hukumar tana aiki ne tare da hadin gwiwar abokan huldar waje, da suka hada da kungiyar kwararrun na’urar kwamfuta ta Nijeriya, da manyan masu jarrabawa daga manyan makarantu, da kungiyar ilimi da cibiyar bincike a Afirka. Wadannan hadin gwiwar, in ji shi, suna da nufin samar da ingantaccen bincike da kuma sahihin bincike.

“Idan an gano cewa an samu tangarda a na’ura, to za a dauki matakan gyarawa ba tare da bata wani lokaci ba,” Benjamin ya tabbatar.

Duk da wannan tabbacin da aka bayar, sama da dalibai 8,000 ne suka shigar da korafinsu a hukumance suna cewa an samu matsaloli na na’ura sosai a yayin jarabawa. Abubuwan da aka ruwaito sun hada da daskararrun allon kwamfuta, jinkirin shiga cikin tsarin zana jarabawar daga ita kwanfutar, da karewar zaman jarrabawa ba zato ba tsammani.

Binciken farko na sakamakon UTME na 2025 ya nuna cewa sama da kashi 78 na sama da dalibai miliyan 1.9 sun samu maki kasa da 200 cikin matsakaicin maki 400. Alkaluman sun kara zurfafa shakku na gazawar fasaha ko na tsari.

Benjamin ya ce duk da haka, lamarin ya tsaya kan sakamakon kamar yadda aka fitar a halin yanzu, yana mai bayyana cewa sun yi daidai da hakikanin kwazon da dalibai suka nuna. Har ila yau, ya amince da alhakin hukumar ta binciki duk rahotannin da suka dace na abubuwan da suka faru.

Sai dai hukumar ta nemi a kwantar da hankali har zuwa lokacin da za ta kammala binciko shin an samu matsala a tsarin jarabawar ko kuma gazawar kwazon ɗalibai ne.

JAMB
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
Ilimi

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

May 31, 2026
Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
Ilimi

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

May 30, 2026
Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
Bakon Marubuci

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

May 27, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.