• English
  • Business News
Tuesday, September 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Buƙaci Hukumomi Da Ma’aikatu Kan Yin Aiki Tuƙuru Dan Kishin Ƙasa

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Minista Ya Buƙaci Hukumomi Da Ma’aikatu Kan Yin Aiki Tuƙuru Dan Kishin Ƙasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya rattaba hannu kan yarjejeniyar yin aiki tuƙuru tare da shugabannin hukumomi da ƙungiyoyin da ke ƙarƙashin ma’aikatarsa.

 

Ministan ya umarce su da su yi aiki wurjanjan domin yaɗa bayanai kan nasarorin Shirin Sabunta Fata na Shugaban Ƙasa Bola Tinubu.

  • Shirin 3MTT Zai Samar Wa Matasa Miliyan Uku Aikin Yi, inji Ministan Yaɗa Labarai
  • Kungiyar Likitoci Ta Kasa Ta Yi Barazanar Tsunduma Yajin Aiki Kan Sace Abokiyar Aikinsu

Idris ya yi wannan kiran ne a Abuja ranar Talata yayin da yake buɗe taron kwana ɗaya na Daraktocin Ma’aikatar da shugabannin hukumomin ta da cibiyoyin ta.

 

Labarai Masu Nasaba

Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja

Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye

Ya ce, “Tun zuwan gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, akwai tsarin da aka yi don cimma Shirin Sabunta Fata tare da dukkanin ma’aikatu da hukumomi, tare da kuma na’urar bin diddigi don tabbatar da ɗa’a. Sashen Bayarwa da Gudanar da Sakamako (CRDCU) a ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya ne ke sarrafa na’urar bin diddigin.

 

“Dukkan ku a nan kuna da alhakin kai sakamakon mu ga wannan ofishi a matsayin shugabanni ko Jami’an Bayarwa. An shirya wannan taro ne don tabbatar da cewa mun fahimci wannan alhakin.

 

“Za ku iya tuna cewa ni da Babbar Sakatariya mun rattaba hannu kan yarjejeniyar aiki tuƙuru tare da Shugaban Ƙasa don tabbatar da cewa za mu aiwatar da aikin ma’aikatar. An gaya mani cewa Babbar Sakatariya ta sa daraktoci su ma su jajirce wajen aiwatar da aikin.

 

“A yayin wannan taron, na yi ƙudiri aniyar samun shugabannin hukumomi su sanya hannu kan yarjejeniyar aiki tuƙuru su ma.”

 

Ministan ya bayyana cewa akwai buƙatar shugabannin hukumomin yaɗa labarai da sassan ma’aikatar su fahimci ƙoƙarin gwamnati na shirin Sabunta Fata. Wannan ya haɗa da haɓaka mafi ƙarancin albashi, lamunin ɗalibai, rance na mabuƙaci, lamunin kasuwanci, da tallafi daban-daban, ta yadda za su iya isar da bayanai kan waɗannan ga jama’a yadda ya kamata.

 

“Har ila yau, gwamnati ba ta bar ayyukan ta na samar da ababen more rayuwa da ayyukan jama’a a faɗin ƙasar nan ba; dole ne mu fahimci wannan yunƙurin kafin mu iya yaɗa su cikin nasara,” inji shi.

 

Idris ya ce ayyukan ma’aikatar har ila yau sun haɗa da ayyukan da suka shafi tsari da haɗa kai da sauran hukumomin gwamnati don yaɗa bayanan ayyukan su.

 

Ya buƙaci mahalarta taron da su tattauna game da wuraren da ba su da tabbas don tabbatar da cewa ba wai kawai sun aiwatar da aikin su tuƙuru ba, a’a har ma a riƙa ganin sun yi hakan yadda ya kamata.

 

Idris ya kuma miƙa godiyar sa ga Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara ta Musamman kan Tsare-tsare, Hadiza Bala Usman, bisa yadda ta nuna sha’awar ta kan wannan aiki, ya kuma yaba da irin kyakkyawan aikin da tawagar ta ke yi a CRDCU.

 

Mahalarta taron sun haɗa da Babbar Sakatariyar Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Dakta Ngozi Onwudiwe; Darakta Janar na hukumar talabijin ta NTA, Comrade Abdulhameed Dembos; Darakta Janar na Hukumar Kula da Gidajen Talabijin da Rediyo ta Ƙasa (NBC), Mista Charles Ebuebu; Darakta Janar na Hukumar Rediyon Tarayyar Nijeriya (FRCN), Dakta Mohammed Bulama; Darakta Janar na gidan rediyon Muryar Nijeriya (VON), Malam Jibrin Baba Ndace; Manajan Darakta na Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN), Alhaji Ali Mohammed Ali, Sakatariyar Zartaswa ta Majalisar Jarida ta Nijeriya, Dakta Dili Ezughah; da daraktoci a ma’aikatar, da sauran su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shirin Tsaftace Ruwa Na Sin Ya Lashe Lambar Karramawa Ta Kasa Da Kasa A Fannin Kirkire Kirkire

Next Post

Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Related

Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja
Labarai

Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja

1 hour ago
Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye
Manyan Labarai

Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye

3 hours ago
Kotu Ta Umarci A Kamo Mata Dogarin Gwamna El-Rufa’i
Labarai

El-Rufa’i Ya Shigar Da Ƙara Kan Zargin Ƴansanda Da Cin Zarafinsa A Kaduna

5 hours ago
Gwamnatin Jigawa Ta Dage Komawa Makaranta Saboda Kidayar Jama’a
Manyan Labarai

Gini Ya Rushe A Jigawa, Mutum 1 Ya Rasu, 7 Sun Jikkata

6 hours ago
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kai Hare-hare 261, ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 1,950 A Watan Agusta – NOA

15 hours ago
'yansanda
Labarai

An Kama Mutane 30 Da Zargin Laifin Aikin Dabanci A Yayin Zagayen Maulidi A Neja

16 hours ago
Next Post
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

LABARAI MASU NASABA

Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja

Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja

September 9, 2025
Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein

Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein

September 9, 2025
Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye

Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye

September 9, 2025
Kotu Ta Umarci A Kamo Mata Dogarin Gwamna El-Rufa’i

El-Rufa’i Ya Shigar Da Ƙara Kan Zargin Ƴansanda Da Cin Zarafinsa A Kaduna

September 9, 2025
Gwamnatin Jigawa Ta Dage Komawa Makaranta Saboda Kidayar Jama’a

Gini Ya Rushe A Jigawa, Mutum 1 Ya Rasu, 7 Sun Jikkata

September 9, 2025
Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

September 8, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Kai Hare-hare 261, ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 1,950 A Watan Agusta – NOA

September 8, 2025
Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

September 8, 2025
'yansanda

An Kama Mutane 30 Da Zargin Laifin Aikin Dabanci A Yayin Zagayen Maulidi A Neja

September 8, 2025
Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

September 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.