• English
  • Business News
Tuesday, November 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Kaddamar Da Taron Horas Da ‘Yan Jarida Kan Yaƙi Da Aƙidun Ta’addanci

by Sulaiman
1 year ago
Minista

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ƙaddamar da taron horas da ‘yan jarida na kwana biyu kan inganta rahotonni domin daƙile aƙidar ta’addanci.

An buɗe taron ne a ranar Talata a Abuja a Ofishin Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Harkokin Tsaro (ONSA), Malam Nuhu Ribadu.

  • Abu Ɗaya Da Ya Rage Kafin Yanke Hukunci Kan Mafi Ƙarancin Albashi
  • Za Mu Canza Salon Yaƙin Da Muke Yi Da Ƴan Bindiga a Nijeriya – Bola Tunibu

A jawabinsa, Idris ya yaba wa Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci ta Ƙasa (NCTC) da ONSA bisa irin ingantattun matakan da suka ɗauka na yaƙi da ta’addanci, ciki har da ayyukan ceto da dama da ba a bayyana ba.

Ya bayyana muhimmancin sadarwar da kafafen yaɗa labarai da suke yi a kai a kai, wanda hakan ke taimaka wa jama’a su fahimci al’amuran ta’addanci da tsaron ƙasa.

Ya ce: “Kafofin yaɗa labarai na da ƙarfi sosai wajen yin tasiri ga mutane da kuma inganta zaman lafiya.”

LABARAI MASU NASABA

Obasanjo Ya Buƙaci Matasa Su Karɓi Ragamar Shugabanci A Ƙasashen Afrika

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 A Ƙauyen Katsina

Ministan ya jaddada cewa ko dai ‘yan jarida na iya cutarwa ko kuma su taimaka wajen yaƙi da tsauraran aƙidu inda ya ƙara da cewa kyakkyawan rahoto zai iya ilimantar da jama’a domin su guje wa ta’addanci.

Ya buƙaci ‘yan jarida da su riƙa ba da sahihan labarai da ke cin karo da saƙwannin ‘yan ta’adda da kuma nuna nasarorin shirye-shiryen NCTC da ONSA waɗanda ke taimakawa wajen hana tayar da zaune tsaye da sake dawo da tsofaffin ‘yan ta’adda.

Ya kuma buƙaci ‘yan jarida da su yi aiki tare da masana harkokin tsaro, masana ilimin zamantakewa, masana ilimin halayyar ɗan’adam, da shugabannin al’umma don samar da ra’ayi mabambanta game da ta’addanci da hanyoyin sa.

Idris ya ce yin amfani da bayanai da bincike na iya sa labaran su su zama abin dogaro.

Ya sake jaddada goyon bayan Gwamnatin Tinubu ga aikin jarida, tare da yin alƙawarin ci gaba da bayar da sahihan bayanai na yau da kullum, da damarmarkin horaswa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Rashin Aiki Ga Matasa Babbar Barazana Ce Ga Nijeriya – Obasanjo 
Manyan Labarai

Obasanjo Ya Buƙaci Matasa Su Karɓi Ragamar Shugabanci A Ƙasashen Afrika

November 11, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 A Ƙauyen Katsina

November 11, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

November 10, 2025
Next Post
Li Qiang: Sin Za Ta Samar Da Karin Dama Da Yanayi Mai Kyau Ga Masu Zuba Jari Na Kasa Da Kasa

Li Qiang: Sin Za Ta Samar Da Karin Dama Da Yanayi Mai Kyau Ga Masu Zuba Jari Na Kasa Da Kasa

LABARAI MASU NASABA

Rashin Aiki Ga Matasa Babbar Barazana Ce Ga Nijeriya – Obasanjo 

Obasanjo Ya Buƙaci Matasa Su Karɓi Ragamar Shugabanci A Ƙasashen Afrika

November 11, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 A Ƙauyen Katsina

November 11, 2025
An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

November 10, 2025
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

November 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

November 10, 2025
Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa

Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa

November 10, 2025
Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Masu Zagaye Kusa Da Doron Kasa

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Masu Zagaye Kusa Da Doron Kasa

November 10, 2025
Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

November 10, 2025
Binciken Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Ci Gaba Da Bude Kofa Mai Zurfi A Sin

Binciken Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Ci Gaba Da Bude Kofa Mai Zurfi A Sin

November 10, 2025
Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump

Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump

November 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.