• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Kaddamar Da Taron Horas Da ‘Yan Jarida Kan Yaƙi Da Aƙidun Ta’addanci

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Minista Ya Kaddamar Da Taron Horas Da ‘Yan Jarida Kan Yaƙi Da Aƙidun Ta’addanci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ƙaddamar da taron horas da ‘yan jarida na kwana biyu kan inganta rahotonni domin daƙile aƙidar ta’addanci.

An buɗe taron ne a ranar Talata a Abuja a Ofishin Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Harkokin Tsaro (ONSA), Malam Nuhu Ribadu.

  • Abu Ɗaya Da Ya Rage Kafin Yanke Hukunci Kan Mafi Ƙarancin Albashi
  • Za Mu Canza Salon Yaƙin Da Muke Yi Da Ƴan Bindiga a Nijeriya – Bola Tunibu

A jawabinsa, Idris ya yaba wa Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci ta Ƙasa (NCTC) da ONSA bisa irin ingantattun matakan da suka ɗauka na yaƙi da ta’addanci, ciki har da ayyukan ceto da dama da ba a bayyana ba.

Ya bayyana muhimmancin sadarwar da kafafen yaɗa labarai da suke yi a kai a kai, wanda hakan ke taimaka wa jama’a su fahimci al’amuran ta’addanci da tsaron ƙasa.

Ya ce: “Kafofin yaɗa labarai na da ƙarfi sosai wajen yin tasiri ga mutane da kuma inganta zaman lafiya.”

Labarai Masu Nasaba

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Ministan ya jaddada cewa ko dai ‘yan jarida na iya cutarwa ko kuma su taimaka wajen yaƙi da tsauraran aƙidu inda ya ƙara da cewa kyakkyawan rahoto zai iya ilimantar da jama’a domin su guje wa ta’addanci.

Ya buƙaci ‘yan jarida da su riƙa ba da sahihan labarai da ke cin karo da saƙwannin ‘yan ta’adda da kuma nuna nasarorin shirye-shiryen NCTC da ONSA waɗanda ke taimakawa wajen hana tayar da zaune tsaye da sake dawo da tsofaffin ‘yan ta’adda.

Ya kuma buƙaci ‘yan jarida da su yi aiki tare da masana harkokin tsaro, masana ilimin zamantakewa, masana ilimin halayyar ɗan’adam, da shugabannin al’umma don samar da ra’ayi mabambanta game da ta’addanci da hanyoyin sa.

Idris ya ce yin amfani da bayanai da bincike na iya sa labaran su su zama abin dogaro.

Ya sake jaddada goyon bayan Gwamnatin Tinubu ga aikin jarida, tare da yin alƙawarin ci gaba da bayar da sahihan bayanai na yau da kullum, da damarmarkin horaswa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ministan Yaɗa LabaraiNUJYada Labarai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kafa Kananan Rukunoni Ba Zai Haifar Da Komai Ba Face Tsananta Sabani

Next Post

Li Qiang: Sin Za Ta Samar Da Karin Dama Da Yanayi Mai Kyau Ga Masu Zuba Jari Na Kasa Da Kasa

Related

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

4 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

5 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

6 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

7 hours ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

8 hours ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

9 hours ago
Next Post
Li Qiang: Sin Za Ta Samar Da Karin Dama Da Yanayi Mai Kyau Ga Masu Zuba Jari Na Kasa Da Kasa

Li Qiang: Sin Za Ta Samar Da Karin Dama Da Yanayi Mai Kyau Ga Masu Zuba Jari Na Kasa Da Kasa

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.