• English
  • Business News
Thursday, July 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Nemi ‘Yan Kasuwa Su Zuba Jari Don Habaka Kasuwancin Iskar Gas Na CNG

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Minista Ya Nemi ‘Yan Kasuwa Su Zuba Jari Don Habaka Kasuwancin Iskar Gas Na CNG
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi kira ga ‘yan kasuwa da su kasance kan gaba a shirin Gwamnatin Tarayya na yin amfani da Iskar Gas (CNG) a Nijeriya. 

Hadimin Musamman kan Yaɗa Labarai na ministan, Malam Rabi’u Ibrahim, ya faɗa a cikin wata sanarwa ga manema labarai cewa, ministan ya furta haka ne a ranar Talata a Abuja a wurin ƙaddamar da masana’antar iskar gas ta ABG CNG tare da yaye injiniyoyin 40 da su ka ƙware a harkar sarrafa CNG.

  • Jerin Jami’o’i 18 Da NUC Ta Haramta Karatu Acikinsu
  • Cire Tallafin Fetur: Kano Za Ta Biya Ma’aikata Karin Albashin N20,000, ‘Yan Fansho N15,000.

Idris ya ce wannan ƙoƙari da rukunin kamfanonin ABG Group ya yi abu ne wanda ya dace kuma ya zo a kan kari.

Haka kuma ya ce amfani da matsattsiyar iskar gas wani abu ne wanda ya zo kenan kuma shi ne hanyar rage kashe kuɗi a ɓangaren harkar sufuri.

Idris ya yaba wa Shugaban Ƙasa Bola Tinubu kan yadda ya jagoranci yadda za a koma ana amfani da iskar gas ta CNG a maimakon man fetur a motocin haya da ƙanana na shiga.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato

Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa

Ya ce: “Iskar gas ta CNG ita ce za a riƙa amfani da ita nan gaba, don haka ya na da muhimmanci ga ‘yan kasuwa a Nijeriya su yi amfani da wannan damar ta shirin gwamnati kan CNG ɗin ta hanyar zuba jari na ɗaukar ma’aikata da sayen kayan aiki da ake buƙata don haɓaka sashen a duk faɗin Nijeriya.”

Ministan ya bayyana cewa ya zuwa yanzu har gwamnatin Tinubu ta kasafta naira biliyan 100 a matakin farko ga harkar gas ɗin CNG, kuma ma har ga shi Ƙungiyar Ƙwadago ta Nijeriya (NLC) ta yi na’am da shirin CNG ɗin wanda hakan ya taimaka wajen sanyin da ta yi kan maganar da ke tsakanin ta da Gwamnatin Tarayya.

Shugaban rukunin kamfanonin ABG Group, Alhaji Bawa Garba, a nasa jawabin, ya ce amfani da iskar gas ta CNG wani maganin matsala ne salin alin wanda ya ke buƙatar goyon baya da ciniki daga gwamnati idan har ana so ya faɗaɗa har a riƙa yi wa Nijeriya kallon “Ƙasar Iskar Gas.”

CNG Ya ce: “Kamfanin mu ya na godiya ga Shugaba Tinubu saboda bajintar da ya yi wajen yanke shawarar a riƙa yin amfani da CNG. Mu da ma can kamfani ne wanda ke fara yin abu, don haka shaidar shigar mu cikin tsarin CNG ita ce yadda mu ka horas da ɗimbin injiniyoyin sauya CNG a faɗin Nijeriya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaCNGMinistan Yaɗa Labarai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mutane 6,000 Sun Amfana Da Zakka Ta Miliyan N132 A Masarautar Hadejia – Kakakin Masarautar 

Next Post

Zargin Sata: Jami’an ‘Yansanda A Kaduna Sun Kama Buhunan Taki Guda 600

Related

Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato

33 minutes ago
Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa
Labarai

Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa

3 hours ago
Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC
Manyan Labarai

Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

5 hours ago
Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara
Labarai

Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara

6 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet

7 hours ago
Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila
Manyan Labarai

Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila

9 hours ago
Next Post
Taki

Zargin Sata: Jami’an ‘Yansanda A Kaduna Sun Kama Buhunan Taki Guda 600

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato

Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato

July 17, 2025
Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa

Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa

July 17, 2025
Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

July 17, 2025
Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara

July 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet

July 17, 2025
Alkaluman Tattalin Arzikin Sin A Rabin Farkon Bana Sun Zarce Hasashen Da Aka Yi

Alkaluman Tattalin Arzikin Sin A Rabin Farkon Bana Sun Zarce Hasashen Da Aka Yi

July 17, 2025
Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila

Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila

July 17, 2025
Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu

Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu

July 17, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kafa Makomar Halittun Duniya Ta Bai Daya

Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kafa Makomar Halittun Duniya Ta Bai Daya

July 16, 2025
Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi

July 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.