ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Nemi ‘Yan Kasuwa Su Zuba Jari Don Habaka Kasuwancin Iskar Gas Na CNG

by Sulaiman
2 years ago
CNG

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi kira ga ‘yan kasuwa da su kasance kan gaba a shirin Gwamnatin Tarayya na yin amfani da Iskar Gas (CNG) a Nijeriya. 

Hadimin Musamman kan Yaɗa Labarai na ministan, Malam Rabi’u Ibrahim, ya faɗa a cikin wata sanarwa ga manema labarai cewa, ministan ya furta haka ne a ranar Talata a Abuja a wurin ƙaddamar da masana’antar iskar gas ta ABG CNG tare da yaye injiniyoyin 40 da su ka ƙware a harkar sarrafa CNG.

  • Jerin Jami’o’i 18 Da NUC Ta Haramta Karatu Acikinsu
  • Cire Tallafin Fetur: Kano Za Ta Biya Ma’aikata Karin Albashin N20,000, ‘Yan Fansho N15,000.

Idris ya ce wannan ƙoƙari da rukunin kamfanonin ABG Group ya yi abu ne wanda ya dace kuma ya zo a kan kari.

ADVERTISEMENT

Haka kuma ya ce amfani da matsattsiyar iskar gas wani abu ne wanda ya zo kenan kuma shi ne hanyar rage kashe kuɗi a ɓangaren harkar sufuri.

Idris ya yaba wa Shugaban Ƙasa Bola Tinubu kan yadda ya jagoranci yadda za a koma ana amfani da iskar gas ta CNG a maimakon man fetur a motocin haya da ƙanana na shiga.

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Ya ce: “Iskar gas ta CNG ita ce za a riƙa amfani da ita nan gaba, don haka ya na da muhimmanci ga ‘yan kasuwa a Nijeriya su yi amfani da wannan damar ta shirin gwamnati kan CNG ɗin ta hanyar zuba jari na ɗaukar ma’aikata da sayen kayan aiki da ake buƙata don haɓaka sashen a duk faɗin Nijeriya.”

Ministan ya bayyana cewa ya zuwa yanzu har gwamnatin Tinubu ta kasafta naira biliyan 100 a matakin farko ga harkar gas ɗin CNG, kuma ma har ga shi Ƙungiyar Ƙwadago ta Nijeriya (NLC) ta yi na’am da shirin CNG ɗin wanda hakan ya taimaka wajen sanyin da ta yi kan maganar da ke tsakanin ta da Gwamnatin Tarayya.

Shugaban rukunin kamfanonin ABG Group, Alhaji Bawa Garba, a nasa jawabin, ya ce amfani da iskar gas ta CNG wani maganin matsala ne salin alin wanda ya ke buƙatar goyon baya da ciniki daga gwamnati idan har ana so ya faɗaɗa har a riƙa yi wa Nijeriya kallon “Ƙasar Iskar Gas.”

CNG Ya ce: “Kamfanin mu ya na godiya ga Shugaba Tinubu saboda bajintar da ya yi wajen yanke shawarar a riƙa yin amfani da CNG. Mu da ma can kamfani ne wanda ke fara yin abu, don haka shaidar shigar mu cikin tsarin CNG ita ce yadda mu ka horas da ɗimbin injiniyoyin sauya CNG a faɗin Nijeriya.”

CNG
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • Sulaiman
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Next Post
Taki

Zargin Sata: Jami’an ‘Yansanda A Kaduna Sun Kama Buhunan Taki Guda 600

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.