• English
  • Business News
Friday, May 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Sake Jaddada Ƙudirin Sabunta Kayan Aikin Watsa Labarai Na Gwamnati

by Sulaiman
1 month ago
in Labarai
0
Minista Ya Sake Jaddada Ƙudirin Sabunta Kayan Aikin Watsa Labarai Na Gwamnati
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya sake jaddada aniyar Gwamnatin Tarayya ta sabuntawa da kuma inganta dukkanin kayan aikin watsa labarai na gwamnati, a wani ɓangare na ƙoƙarin ta na gyara fagen yaɗa labarai a Nijeriya.

 

Mai taimaka wa ministan kan harkokin yaɗa labarai, Rabi’u Ibrahim, ya faɗa a cikin takarda ga manema labarai cewa Ministan ya bayyana haka ne a ranar Alhamis, yayin da yake jawabi a Zauren Taron Manema Labarai da Ministoci na Shekarar 2025, karo na shida, wanda aka gudanar a Cibiyar ‘Yan Jarida ta Ƙasa da ke Abuja.

  • Xi: Daukar Matsayar Kashin Kai Da Danniya Ba Za Su Taba Samun Goyon Bayan Al’umma Ba
  • Boko Haram Sun Kashe Sojoji 2 Da Wasu A Wani Sabon Hari A Borno

Ministan, wanda bai daɗe da dawowa daga Babban Taro Da Bita na Ƙungiyar Masu Watsa Labarai ta Ƙasa (NAB) da aka gudanar a birnin Las Vegas na ƙasar Amurka ba, ya ce taron – mai taken “Fasaha, Madosa, Makoma” – ya ƙunshi musayar ra’ayoyi daga ƙwararru a fannin fasaha da watsa labarai daga sassa daban-daban na duniya.

 

Labarai Masu Nasaba

‘Yan PDP Na Komawa APC Ne Saboda Jam’iyyarsu Na Jin ƙamshin Mutuwa – Ganduje

Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Waɗanda suka take wa Ministan sawu a tafiyar su ne jagororin hukumomin yaɗa labarai da wayar da kai da ke ƙarƙashin ma’aikatar sa.

Ya yi zama daban-daban tare da ƙwararru inda suka tattauna kan yadda za a inganta ƙwarewa da kuma kayan aiki na zamani na kafafen yaɗa labarai na gwamnatin Nijeriya.

 

Ya ce: “Ina sanar da ku waɗannan abubuwan ne domin jaddada ƙudirin gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu na ganin an samu cigaba mai ɗorewa a fannin watsa labarai a ƙasar nan.

 

“Wannan ne ma ya sanya muke gudanar da irin wannan taron bita na ministoci, da kuma shirin ƙaddamar da Taron Tattaunawa da Jama’a a sassan ƙasar nan nan gaba kaɗan.”

Minista

Idris ya kuma bayyana halartar da ya yi a Taron Kasuwanci na Nijeriya da aka yi a birnin Paris, ƙasar Faransa, wanda kamfanin Business France ya shirya.

 

A gefen taron, Idris ya gana da manyan jami’an hukumar UNESCO domin ƙara inganta shirin kafa Cibiyar Ilimin Kafofin Watsa Labarai a birnin Abuja.

 

A cewar sa, wannan cibiyar za ta taimaka gaya wajen bunƙasa hazaƙar ‘yan jarida da kuma gina sahihin tsarin yaɗa labarai mai inganci a ƙasar nan.

 

Ya ce: “Cibiyar za ta taka muhimmiyar rawa wurin ƙara ƙarfin gwiwa da ingancin aikin ‘yan jarida a Nijeriya.”

 

Idris ya ƙara da cewa shirye-shiryen da ake yi kamar wannan taron bita da kuma Taron Tattaunawa da Jama’a da ke tafe, yana daga cikin dabarun gwamnatin don ƙarfafa gaskiya, ƙarfafa tattaunawa tsakanin gwamnati da al’umma, da kuma ƙarfafa amincewa a tsakanin ɓangarorin biyu.

 

A yayin taron, Ministan Wutar Lantarki, Cif Adebayo Adelabu, ya yi bayani kan matakan da ake ɗauka don gyara ɓangaren wutar lantarki domin tallafa wa shirin gwamnati na bunƙasa masana’antu da tabbatar da isasshiyar wutar lantarki ga ‘yan Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi: Daukar Matsayar Kashin Kai Da Danniya Ba Za Su Taba Samun Goyon Bayan Al’umma Ba

Next Post

2027: Dalilan Da Suka Sa ‘Yan Siyasa Ke Tururuwar Zuwa Gidan Buhari A Kaduna

Related

Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano
Labarai

‘Yan PDP Na Komawa APC Ne Saboda Jam’iyyarsu Na Jin ƙamshin Mutuwa – Ganduje

7 hours ago
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 
Labarai

Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

9 hours ago
Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 
Manyan Labarai

Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 

10 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

INEC Ta Samar Da Sashen Ƙirƙirarriyar Basira Domin Inganta Harkokin Zaɓe 

12 hours ago
Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya
Ra'ayi Riga

Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya

12 hours ago
Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi
Labarai

Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi

13 hours ago
Next Post
2027: Dalilan Da Suka Sa ‘Yan Siyasa Ke Tururuwar Zuwa Gidan Buhari A Kaduna

2027: Dalilan Da Suka Sa ‘Yan Siyasa Ke Tururuwar Zuwa Gidan Buhari A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Sun Kammala Aiki A Wajen Tashar Sararin Samaniyar Kasar Sin

‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Sun Kammala Aiki A Wajen Tashar Sararin Samaniyar Kasar Sin

May 22, 2025
Ba Zai Yiwu Amurka Ta Kafawa Chips Kirar Kasar Sin Wani Shinge Ba

Ba Zai Yiwu Amurka Ta Kafawa Chips Kirar Kasar Sin Wani Shinge Ba

May 22, 2025
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

‘Yan PDP Na Komawa APC Ne Saboda Jam’iyyarsu Na Jin ƙamshin Mutuwa – Ganduje

May 22, 2025
Masanan Najeriya Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwar Afirka Da Sin A Fannin Tinkarar Kalubalen Harajin Kwastam Na Amurka

Masanan Najeriya Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwar Afirka Da Sin A Fannin Tinkarar Kalubalen Harajin Kwastam Na Amurka

May 22, 2025
Modric Zai Bar Real Madrid Bayan Kammala Gasar Cin Kofin Duniya Na Kungiyoyi

Modric Zai Bar Real Madrid Bayan Kammala Gasar Cin Kofin Duniya Na Kungiyoyi

May 22, 2025
Yawan Wutar Lantarkin Da Sin Ke Iya Samar Ta Amfani Da Karfin Ruwa Ta Kai Matsayin Koli A Duniya

Yawan Wutar Lantarkin Da Sin Ke Iya Samar Ta Amfani Da Karfin Ruwa Ta Kai Matsayin Koli A Duniya

May 22, 2025
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

May 22, 2025
Darussan Koyi Daga Salon Bunkasa Kasa Na Sin

Darussan Koyi Daga Salon Bunkasa Kasa Na Sin

May 22, 2025
Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 

Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 

May 22, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Faransa

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Faransa

May 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.