ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Dalilan Da Suka Sa ‘Yan Siyasa Ke Tururuwar Zuwa Gidan Buhari A Kaduna

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
Siyasa

Yayin da har yanzu ya rage shekaru biyu a gudanar da zaben shugaban kasa a 2027, ‘yan siyasa na ci gaba da gudanar da dubarun siyasa ciki har da tarurruka da kuma ziyarar gidan tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, wanda yanzu ake gani a matsayin sabuwar amarya a fagen siyasar Nijeriya.

Duk da yake gudanar da tarurrukan sun dade suna cikin dubarun siyasar Nijeriya, yanayin da ‘yan siyasa daga jam’iyyar APC mai mulki da ‘yan adawa ke yin safa da marwa zuwa gidan tsohon shugaban kasa a Kaduna don tattaunawar sirri da daukar hotuna tare da shi. Wannan ya faru ne saboda yadda Buhari ya yi watsi da siyasa da kuma karkatar da ‘yan siyasa daga inda suka saba.

  • Manchester Ta Kai Zagayen Semi Final A Europa Bayan Doke Lyon
  • Bai Wa Shanu Guba: Sojoji Sun Shiga Tsakani Domin Dakile Yunkurin Ramuwar Gayya A Filato

Wadannan ziyarar ta kwanan nan ga Buhari, duk da cewa galibi ana alakan ta shi ga neman mulki, wanda ‘yan siyasa suka rike a matsayin wani dubarun neman iko.

ADVERTISEMENT

Har zuwa yanzu ana ganin Buhari ya rabu da siyasar bayan ya bar ofis, Buhari a hankali ya zama mutum mai tallata ‘yan siyasa, inda bangarori daban-daban suna neman goyon bayansa da albarkarsa. Sauya sheka tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, zuwa jam’iyyar SDP ya kara tsananta jita-jita game da ra’ayin siyasar tsohon shugaban a yanzu.

Don haka, lokacin da tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, wanda kwanan nan ya sanar da kwancen hadin gwiwar jam’iyyun adawa don hambarar da Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya jagoranci gungun manyan ‘yan siyasa ciki har da El-Rufai da tsohon gwamnan Jihar Sakkwato, Aminu Tambuwal zuwa gidan Buhari a Kaduna, masu sharhi da yawa sun fassara hakan a matsayin wata magana a fili ga tsohon shugaban kasar. An bayyana cewa makusantarsa ‘yan asalin jam’iyyar CPC suna shirin ficewa daga APC.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

Duk da cewa Atiku ya dage yayin tattaunawar da ya yi da manema labarai bayan ziyarar cewa ganawar ba ta batun siyasa ba ne, amma jawabin El-Rufai ya nuna karara akwai siyasa a cikin ganawar.

Bayan ziyarar ‘yan adawa kwanaki kadan da na gwamnonin APC, shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya isa gidan Buhari sa’o’i kadan bayan tawagar Atiku, wanda ya kara tsananta siyasa. Ya kuma ba da tabbaci ga ra’ayin cewa shugabannin jam’iyyar APC sun damu da siyasar tsohon shugaban kasar.

Masu lura da al’amura siyasa sun bayyana cewa kalaman da Ganduje ya yi bayan ganawar, ya tabbatar da cewa APC na yin duk mai yiwuwa wajen tabbatar da cewa Buhari ya kasance tare da jam’iyya mai mulki. Wannan matakin na zuwa ne yayin da kawancen ‘yan adawa ke samun karfi, musamman a yayin da ake zaman doya da manja tsakanin gwamnatin Tinubu da ‘yan arewa.

Idan za a iya tunawa a lokacin watan Ramadan, dan shugaban kasa, Seyi Tinubu ya kai ziyarar girmamawa ga Buhari da sauran shugabannin siyasar arewa a lokacin rangadin da ya kai yankin.

Mai sharhi kan harkokin siyasa, Shamsudeen Ibrahim ya bayyana ziyarar da kwamitin gudanarwa na APC da Ganduje ke jagoranta suka kai ga Buhari a matsayin tsoron rasa riko, tsoron rasa arewa, da tsoron rarrabuwar kawuna. Ba ziyarar ‘yan’uwantaka ba ne. Ziyarar neman tsira ne.

Mai sharhi kan harkokin jama’a, Dakta Saidu Dukawa, ya kara da cewa ziyarar ta zama wata manuniya ga jama’a cewa shirye-shiryen zaben 2027.

Dukawa, ya kasance babban malami a jami’ar Bayero da ke Kano (BUK), ya ce, “A bayana, ana yin irin wannan ziyarar ga tsoffin shugabannin kasa da suka hada da Obasanjo da Jonathan don cimma manufofin siyasa, amma yanzu lamarin ya zama tarihi. “

Siyasa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Siyasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
An Gudanar Da Bikin Musanyar Al’Adun Al’ummun Sin Da Cambodia A Phnom Penh

An Gudanar Da Bikin Musanyar Al’Adun Al’ummun Sin Da Cambodia A Phnom Penh

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.