• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Yaba Da Yadda Aka Gudanar Da Zaɓen Kungiyoyin IPI Da NUJ

by Sulaiman
6 months ago
in Labarai
0
Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yaba wa Cibiyar ‘Yan Jarida ta Duniya (IPI) da Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Nijeriya (NUJ) bisa nasarar gudanar da zaɓukan sababbin shugabannin su.

 

A cikin wata sanarwa da ya fitar, Ministan ya taya murna ga Musikilu Mojeed, shugaban kamfanin jaridar onlayin ta Premium Times, da Ahmed Shekarau, Manajan Daraktan kamfanin Media Trust, kan sake zaɓen su da aka yi a matsayin Shugaba da Sakatare, bi da bi, tare da wasu jami’ai huɗu da aka sake zaɓa.

  • Kaduna: Gwamnatin Tarayya Ta Fara Sayar Wa ‘Yan Jarida Buhun Shinkafa A Kan Naira 40,000
  • Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Muhimmiyar Makalar Xi Mai Taken “Zurfafa Aiwatar Da Juyin Juya Halin Jam’iyyar Kwaminis Ta Sin”

Ya ce: “Ina taya Malam Musikilu Mojeed, Shugaban kamfanin Premium Times, da Ahmed Shekarau, Manajan Darakta na Media Trust, waɗanda aka sake zaɓen su a matsayin Shugaba da Sakatare, bi da bi, da kuma sake zaɓen wasu jami’ai guda huɗu na IPI reshen Nijeriya.”

 

Labarai Masu Nasaba

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Ministan ya kuma yaba wa sauyin shugabanci cikin lumana da ake yi a NUJ, wanda ya haifar da zaɓen Malam Alhassan Yahaya a matsayin Shugaba da kuma Abimbola Oyetunde a matsayin mace ta farko da ta zama Mataimakiyar Shugaban ƙungiyar ta ƙasa.

 

Har ila yau, Idris ya yaba wa gwamnatin Jihar Imo saboda rawar da ta taka wajen gudanar da zaɓen na NUJ.

 

Ya ce: “Dole ne in yaba wa gwamnatin Jihar Imo kan goyon bayan da ta bayar da kuma karimcin ta wajen karɓar baƙuncin membobi da wakilan NUJ, wanda ya taimaka wajen samun nasarar zaɓen.”

 

Daga nan ya yi kira ga IPI da NUJ da su ci gaba da jajircewa wajen inganta aikin jarida yadda ya dace.

 

Ya ce: “A matsayin ku na masu kare gaskiya, dole ne ‘yan jarida su ba da fifiko ga gaskiya da riƙon amana a cikin aikin su. Ina kira ga ƙungiyoyin biyu da su tabbatar da cewa membobin su suna bin mafi kyawun ƙa’idojin aikin jarida don inganta dimokiraɗiyyar mu.”

 

Ministan ya kuma jaddada cewa gwamnati za ta ci gaba da kare ‘yancin ‘yan jarida, inda ya ce, “Za mu ci gaba da kare haƙƙoƙin ‘yan jarida, ta yadda za a tabbatar da yanayi mai kyau don aikin jarida ya bunƙasa a Nijeriya.”

 

Ita dai Cibiyar ‘Yan Jarida ta Duniya, wato International Press Institute (IPI), wata ƙungiya ce ta duniya da ke ƙunshe da ‘yan jarida, editoci, da shugabannin kafafen yaɗa labarai da suka himmatu wajen kare ‘yancin ‘yan jarida da inganta aikin jarida mai zaman kan sa da bambancin kafafen yaɗa labarai a duniya baki ɗaya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Sauya Sunan Jami’ar Abuja Zuwa Jami’ar Yakubu Gowon

Next Post

Firaminista Li Qiang Ya Shugabanci Taron Majalisar Gudanarwar Kasar Sin

Related

An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

6 minutes ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

2 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

3 hours ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

4 hours ago
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano
Labarai

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

4 hours ago
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato
Labarai

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

8 hours ago
Next Post
Firaminista Li Qiang Ya Shugabanci Taron Majalisar Gudanarwar Kasar Sin

Firaminista Li Qiang Ya Shugabanci Taron Majalisar Gudanarwar Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

June 28, 2025
Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

June 28, 2025
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

June 28, 2025
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.