• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Yaba Da Yadda Aka Gudanar Da Zaɓen Kungiyoyin IPI Da NUJ

by Sulaiman
9 months ago
in Labarai
0
Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yaba wa Cibiyar ‘Yan Jarida ta Duniya (IPI) da Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Nijeriya (NUJ) bisa nasarar gudanar da zaɓukan sababbin shugabannin su.

 

A cikin wata sanarwa da ya fitar, Ministan ya taya murna ga Musikilu Mojeed, shugaban kamfanin jaridar onlayin ta Premium Times, da Ahmed Shekarau, Manajan Daraktan kamfanin Media Trust, kan sake zaɓen su da aka yi a matsayin Shugaba da Sakatare, bi da bi, tare da wasu jami’ai huɗu da aka sake zaɓa.

  • Kaduna: Gwamnatin Tarayya Ta Fara Sayar Wa ‘Yan Jarida Buhun Shinkafa A Kan Naira 40,000
  • Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Muhimmiyar Makalar Xi Mai Taken “Zurfafa Aiwatar Da Juyin Juya Halin Jam’iyyar Kwaminis Ta Sin”

Ya ce: “Ina taya Malam Musikilu Mojeed, Shugaban kamfanin Premium Times, da Ahmed Shekarau, Manajan Darakta na Media Trust, waɗanda aka sake zaɓen su a matsayin Shugaba da Sakatare, bi da bi, da kuma sake zaɓen wasu jami’ai guda huɗu na IPI reshen Nijeriya.”

 

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

Ministan ya kuma yaba wa sauyin shugabanci cikin lumana da ake yi a NUJ, wanda ya haifar da zaɓen Malam Alhassan Yahaya a matsayin Shugaba da kuma Abimbola Oyetunde a matsayin mace ta farko da ta zama Mataimakiyar Shugaban ƙungiyar ta ƙasa.

 

Har ila yau, Idris ya yaba wa gwamnatin Jihar Imo saboda rawar da ta taka wajen gudanar da zaɓen na NUJ.

 

Ya ce: “Dole ne in yaba wa gwamnatin Jihar Imo kan goyon bayan da ta bayar da kuma karimcin ta wajen karɓar baƙuncin membobi da wakilan NUJ, wanda ya taimaka wajen samun nasarar zaɓen.”

 

Daga nan ya yi kira ga IPI da NUJ da su ci gaba da jajircewa wajen inganta aikin jarida yadda ya dace.

 

Ya ce: “A matsayin ku na masu kare gaskiya, dole ne ‘yan jarida su ba da fifiko ga gaskiya da riƙon amana a cikin aikin su. Ina kira ga ƙungiyoyin biyu da su tabbatar da cewa membobin su suna bin mafi kyawun ƙa’idojin aikin jarida don inganta dimokiraɗiyyar mu.”

 

Ministan ya kuma jaddada cewa gwamnati za ta ci gaba da kare ‘yancin ‘yan jarida, inda ya ce, “Za mu ci gaba da kare haƙƙoƙin ‘yan jarida, ta yadda za a tabbatar da yanayi mai kyau don aikin jarida ya bunƙasa a Nijeriya.”

 

Ita dai Cibiyar ‘Yan Jarida ta Duniya, wato International Press Institute (IPI), wata ƙungiya ce ta duniya da ke ƙunshe da ‘yan jarida, editoci, da shugabannin kafafen yaɗa labarai da suka himmatu wajen kare ‘yancin ‘yan jarida da inganta aikin jarida mai zaman kan sa da bambancin kafafen yaɗa labarai a duniya baki ɗaya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Sauya Sunan Jami’ar Abuja Zuwa Jami’ar Yakubu Gowon

Next Post

Firaminista Li Qiang Ya Shugabanci Taron Majalisar Gudanarwar Kasar Sin

Related

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja
Tsaro

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

49 minutes ago
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato
Manyan Labarai

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

1 hour ago
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa
Labarai

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

3 hours ago
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno
Labarai

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

5 hours ago
Labarai

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

7 hours ago
NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai
Manyan Labarai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

8 hours ago
Next Post
Firaminista Li Qiang Ya Shugabanci Taron Majalisar Gudanarwar Kasar Sin

Firaminista Li Qiang Ya Shugabanci Taron Majalisar Gudanarwar Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

September 6, 2025
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

September 6, 2025
Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

September 6, 2025
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

September 6, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

September 6, 2025
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

September 6, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

September 6, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

September 6, 2025
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

September 6, 2025

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.