ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Yaba Da Yadda Aka Gudanar Da Zaɓen Kungiyoyin IPI Da NUJ

by Sulaiman
1 year ago
Minista

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yaba wa Cibiyar ‘Yan Jarida ta Duniya (IPI) da Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Nijeriya (NUJ) bisa nasarar gudanar da zaɓukan sababbin shugabannin su.

 

A cikin wata sanarwa da ya fitar, Ministan ya taya murna ga Musikilu Mojeed, shugaban kamfanin jaridar onlayin ta Premium Times, da Ahmed Shekarau, Manajan Daraktan kamfanin Media Trust, kan sake zaɓen su da aka yi a matsayin Shugaba da Sakatare, bi da bi, tare da wasu jami’ai huɗu da aka sake zaɓa.

ADVERTISEMENT
  • Kaduna: Gwamnatin Tarayya Ta Fara Sayar Wa ‘Yan Jarida Buhun Shinkafa A Kan Naira 40,000
  • Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Muhimmiyar Makalar Xi Mai Taken “Zurfafa Aiwatar Da Juyin Juya Halin Jam’iyyar Kwaminis Ta Sin”

Ya ce: “Ina taya Malam Musikilu Mojeed, Shugaban kamfanin Premium Times, da Ahmed Shekarau, Manajan Darakta na Media Trust, waɗanda aka sake zaɓen su a matsayin Shugaba da Sakatare, bi da bi, da kuma sake zaɓen wasu jami’ai guda huɗu na IPI reshen Nijeriya.”

 

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Ministan ya kuma yaba wa sauyin shugabanci cikin lumana da ake yi a NUJ, wanda ya haifar da zaɓen Malam Alhassan Yahaya a matsayin Shugaba da kuma Abimbola Oyetunde a matsayin mace ta farko da ta zama Mataimakiyar Shugaban ƙungiyar ta ƙasa.

 

Har ila yau, Idris ya yaba wa gwamnatin Jihar Imo saboda rawar da ta taka wajen gudanar da zaɓen na NUJ.

 

Ya ce: “Dole ne in yaba wa gwamnatin Jihar Imo kan goyon bayan da ta bayar da kuma karimcin ta wajen karɓar baƙuncin membobi da wakilan NUJ, wanda ya taimaka wajen samun nasarar zaɓen.”

 

Daga nan ya yi kira ga IPI da NUJ da su ci gaba da jajircewa wajen inganta aikin jarida yadda ya dace.

 

Ya ce: “A matsayin ku na masu kare gaskiya, dole ne ‘yan jarida su ba da fifiko ga gaskiya da riƙon amana a cikin aikin su. Ina kira ga ƙungiyoyin biyu da su tabbatar da cewa membobin su suna bin mafi kyawun ƙa’idojin aikin jarida don inganta dimokiraɗiyyar mu.”

 

Ministan ya kuma jaddada cewa gwamnati za ta ci gaba da kare ‘yancin ‘yan jarida, inda ya ce, “Za mu ci gaba da kare haƙƙoƙin ‘yan jarida, ta yadda za a tabbatar da yanayi mai kyau don aikin jarida ya bunƙasa a Nijeriya.”

 

Ita dai Cibiyar ‘Yan Jarida ta Duniya, wato International Press Institute (IPI), wata ƙungiya ce ta duniya da ke ƙunshe da ‘yan jarida, editoci, da shugabannin kafafen yaɗa labarai da suka himmatu wajen kare ‘yancin ‘yan jarida da inganta aikin jarida mai zaman kan sa da bambancin kafafen yaɗa labarai a duniya baki ɗaya.

Minista
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Next Post
Firaminista Li Qiang Ya Shugabanci Taron Majalisar Gudanarwar Kasar Sin

Firaminista Li Qiang Ya Shugabanci Taron Majalisar Gudanarwar Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.