• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Lashi Takobin Karfafa Hadin Gwiwa Da Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Lashi Takobin Karfafa Hadin Gwiwa Da Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya Talata, manema labarai sun zanta da ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi bayan ganawarsa da shugaban kasar Jamhuriyar Kongo, Denis Sassou Nguesso.

Da aka tambaye shi game da shirye-shiryen da kasar Sin da Jamhuriyar Kongo suke da su a matsayin jagororin dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka na FOCAC, wajen aiwatar da sakamakon taron kolin dandalin da aka gudanar a Beijing bara, Wang wanda har ila yau mamba ne a ofishin siyasa na kwamitin koli na Jamiyyar Kwaminis ta Sin, ya ba da amsar cewa, dandalin FOCAC ya taka muhimmiyar rawa wajen daukaka ci gaban Afirka tare da kyautata jin dadin mutanen yankin.

  • JKS Ta Yi Kira Da A Karfafa Gwiwa Da Jajircewa Wajen Yaki Da Cin Hanci Da Karbar Rashawa
  • An Yi Wa ‘Yansanda 110 Ƙarin Girma A Adamawa

Wang ya zayyano wasu muhimman abubuwa guda uku da za a yi laakari da su wajen aiwatar da sakamakon taron bayan tuntubar juna a tsakanin bangarorin biyu yadda ya kamata.

Da farko, Wang ya ce za a karfafa daidaita dabarun samar da ci gaba da musayar fikira da basirar iya shugabanci a tsakanin juna, da zurfafa amfani da hikimomi da sassan cin moriyar juna domin fadada alakokin kasar Sin da Afirka.

Abu na biyu da za a mayar da hankali a kai in ji Wang Yi, shi ne ci gaba da kara kaimin yaukaka zumunci da hadin gwiwa a tsakanin Sin da Afirka, da kara fito da hanyoyi mafiya dacewa da alakar kasa da kasa, da zama abin koyi ta fuskar hadin gwiwa a tsakanin Afirka da sauran yankunan duniya.

Labarai Masu Nasaba

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Kana na uku, shi ne gano alkiblar da ta fi dacewa a dosa da kuma muhimman ayyukan ci gaba da za a fi dora fifiko a kai, tare da habaka matakan zuba jari da cinikayya tsakanin Sin da Afirka domin samar wa yankin na Afirka da kasuwar hada-hada mai girma, da aiki da fasahohin zamani da ci gaba da zuba jarin zamanantar da yankin ba tare da tangarda ba. (Abdulrazaq Yahuza Jere)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Yusuf Zai Raba Naira Biliyan 3 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Kano

Next Post

Gwamna Yusuf Ya Gargaɗi Kwamishinoninsa Kan Duk Wani Yunƙurin Kawo Rarrabuwar Kai A Majalisar Zartarwar Kano 

Related

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
Daga Birnin Sin

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

8 hours ago
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
Daga Birnin Sin

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

9 hours ago
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

10 hours ago
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari
Daga Birnin Sin

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

11 hours ago
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi
Daga Birnin Sin

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

12 hours ago
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

14 hours ago
Next Post
Gwamna Yusuf Ya Gargaɗi Kwamishinoninsa Kan Duk Wani Yunƙurin Kawo Rarrabuwar Kai A Majalisar Zartarwar Kano 

Gwamna Yusuf Ya Gargaɗi Kwamishinoninsa Kan Duk Wani Yunƙurin Kawo Rarrabuwar Kai A Majalisar Zartarwar Kano 

LABARAI MASU NASABA

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.