• English
  • Business News
Monday, October 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Bayyana Ra’ayin Kasar Kan Rikicin Falasdinu Da Isra’ila

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 weeks ago
Sin

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya bayyana ra’ayin kasar Sin game da rikicin da ake yi yanzu haka tsakanin Falasdinu da Isra’ila a ranar Jumma’a 19 ga wata, yayin wata tattaunawa da ministan harkokin wajen kasar Morocco Nasser Bourita a birnin Beijing.

Yayin da yake nuni da cewa, ya kamata kasashen duniya su hada kai wajen tunkarar halin gaggawa da ake ciki a yanzu, Wang ya ce, ya zama wajibi a karfafa tsagaita bude wuta a zirin Gaza tare da daukar matakin gaggawa don magance bala’in tabarbarewar jin kai da ake fuskanta a halin yanzu.

Wang ya ce, dole ne a aiwatar da ka’idar bar “Falasdinawa su mulki Falasdinu” a kan turbar gaskiya. Kuma Gaza da yammacin gabar kogin Jordan duk yankuna ne na Falasdinu da ba za a iya raba su ba. Sannan ya kamata duk wani tsarin shugabanci da na sake gina yankin bayan yaki ya mutunta ra’ayin al’ummar Falasdinu tare da kare halastattun hakkokin kasar Falasdinu.

Wang ya kuma jaddada wajibcin tsayawa tsayin daka kan shawarar kafa kasashe biyu masu cin gashin kansu, da kara cimma matsaya guda daya a tsakanin kasa da kasa, da samar da wani matsayi na bai daya. Wang ya kuma yi kira da a mara baya ga zamowar Falasdinu cikakkiyar mamba a Majalisar Dinkin Duniya bisa amincewa da ita a matsayin kasar Falasdinu mai cin gashin kanta, da neman hanyoyin da za a bi don karfafa tabbatar da kafuwar kasashe biyu, da yin watsi da duk wani mataki na wani bangare guda da zai kawo cikas ga shawarar kafa kasashen biyu. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

 

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya

Ƴan Bindiga Sun Amince Da Dakatar Da Hare-Hare A Ƙananan Hukumomi 5 A Katsina

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya

October 13, 2025
Ƴan Bindiga Sun Amince Da Dakatar Da Hare-Hare A Ƙananan Hukumomi 5 A Katsina
Daga Birnin Sin

Ƴan Bindiga Sun Amince Da Dakatar Da Hare-Hare A Ƙananan Hukumomi 5 A Katsina

October 12, 2025
Kasar Sin Ta Kare Matakinta Na Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Kare Matakinta Na Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth

October 12, 2025
Next Post
Sin

Yadda Ƴan Agbero’ Ke Cin Karensu Ba Babbaka A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

October 13, 2025
Magance Bala’o’i: Gwamna Lawal Ya Jaddada Ƙudirin Gwamnatin Zamfara Na Ci Gaba Da Haɗin Gwiwa Da NEMA

Magance Bala’o’i: Gwamna Lawal Ya Jaddada Ƙudirin Gwamnatin Zamfara Na Ci Gaba Da Haɗin Gwiwa Da NEMA

October 13, 2025
Asuu

Ba Bu Dalilin Da ASUU Za Ta Fara Yajin Aiki, An Biya Duk Buƙatunsu – Ministan Ilimi 

October 13, 2025
hisba

Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano

October 13, 2025
Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

October 13, 2025
Nijeriya

Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista

October 13, 2025
Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano

Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano

October 13, 2025
nema

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya

October 13, 2025
Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya

Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya

October 13, 2025
Sojojin somaliya

Ta’addanci: Ana Fuskantar Ƙarancin Man Fetur A Mali Sakamakon Datse Hanyoyin Shiga Bamako

October 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.