• English
  • Business News
Saturday, May 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Lafiya Ya Yi Alƙawarin Inganta Tallafi Ga Likitoci A Hajjin 2025

by Bello Hamza
2 months ago
in Labarai
0
Ministan Lafiya Ya Yi Alƙawarin Inganta Tallafi Ga Likitoci A Hajjin 2025
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Lafiya da Walwalar Jama’a, Farfesa Muhammad Ali Pate, ya gudanar da wata gagarumar ziyara tare da jami’an Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON) a cibiyoyin kiwon lafiya da ke birnin Makkah, a Saudiyya.

Wannan mataki na nuna jajircewar Gwamnatin Tarayya wajen inganta kiwon lafiyar alhazai.

  • Mutane Miliyan 9 Na Iya Kamuwa Da Cutar HIV Saboda Rashin Tallafi
  • Fursunoni 12 Sun Tsere Daga Gidan Yari A Jihar Kogi

A yayin ziyarar da ya kai ofishin NAHCON a Ummul-Jud, Minista Pate, ya tabbatar da goyon bayan gwamnati domin magance matsalolin kiwon lafiya da alhazai ke fuskanta.

Ya ce wannan shiri na daga cikin ƙudirin Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na inganta jin daɗin mahajjata.

“Sadaukarwarmu tana nan a bayyane,” in ji Minista Pate.

Labarai Masu Nasaba

Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas

“Duba da yanayin kiwon lafiya a duniya tun bayan ɓullar cututtuka kamar sanƙarau da Shan Inna, wajibi ne mu bi ƙa’idojin kiwon lafiya na Saudiyya.

“Dole ne mu tabbatar da cewa dukkanin alhazai sun samu takardun rigakafi da katin shaidar lafiya,” in ji shi.

Ministan, tare da rakiyar wasu manyan jami’an ma’aikatar lafiya, sun duba motocin ɗaukar marasa lafiya na NAHCON, kayan magani, da shirye-shiryen kiwon lafiya a asibitocin Nijeriya da ke Saudiyya.

Sun gano muhimman wuraren da ake buƙatar ingantawa, ciki har da wadatar magunguna, alluran rigakafi, na’urorin likitanci, da motocin ɗaukar marasa lafiya.

Shugaban NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya yaba da shirin Ministan, inda ya ce: “Ziyararku ta ƙara mana ƙwarin gwiwa a ƙoƙarin da muke yi na inganta kiwon lafiyar alhazai.”

A duk shekara, kimanin ‘yan Nijeriya 70,000 ne ke halartar aikin Hajji, kuma Ministan Pate ya bayyana damuwarsa kan matsalolin da ke tattare da yanayin zafi mai tsanani da ake tsammanin fuskanta a Hajjin 2025.

Ya ce an ɗauki matakan kariya don tabbatar da lafiyar alhazai da jin daɗinsu.

Wannan shiri na haɗin gwiwa tsakanin Ma’aikatar Lafiya da NAHCON zai tabbatar da cewa mahajjatan Nijeriya sun samu ingantacciyar kulawa.

NAHCON ta kuma tabbatar da ƙudirinta na ci gaba da samar da ingantattun ayyuka ga alhazai.

Waɗanda suka halarci wannan ziyarar sun haɗa da Minista Pate, Shugaban NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, Kwamishinan Ayyuka Prince Anofi’u Olanrewaju Elegusi, Farfesa Abubakar Abubakar Yagawal, Prince Abdul-Razak Aliyu, Dokta Sa’edu Ahmad Dumbulwa da sauran manyan jami’ai na NAHCON da Ma’aikatar Lafiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlhazaiAlƙawariHajjin 2025Inganta AikiKiwon LafiyaMinista PateNAHCON
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mutane Miliyan 9 Na Iya Kamuwa Da Cutar HIV Saboda Rashin Tallafi

Next Post

An Ɗauko Sojoji Daga Waje Don Horas Da Dakarun Nijeriya 

Related

Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar
Labarai

Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar

11 hours ago
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas

16 hours ago
Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 60 A Borno

17 hours ago
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano
Manyan Labarai

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano

18 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Ƴan Daba 33 A Kano
Labarai

An Kama Mutane 49 Da Ake Zargi Da Damfara A Jihar Kogi

20 hours ago
Duk Da Janye Tallafin Rarar Mai, Matsin Rayuwa Na Addabar ‘Yan Nijeriya
Manyan Labarai

Duk Da Janye Tallafin Rarar Mai, Matsin Rayuwa Na Addabar ‘Yan Nijeriya

22 hours ago
Next Post
An Ɗauko Sojoji Daga Waje Don Horas Da Dakarun Nijeriya 

An Ɗauko Sojoji Daga Waje Don Horas Da Dakarun Nijeriya 

LABARAI MASU NASABA

Darajar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso Shida Bisa Dari A Afirilu

Darajar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso Shida Bisa Dari A Afirilu

May 30, 2025
Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Ta Jiragen Kasa A Sin Na Iya Kaiwa Sama Da Miliyan 80 Yayin Hutun Bikin Duanwu

Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Ta Jiragen Kasa A Sin Na Iya Kaiwa Sama Da Miliyan 80 Yayin Hutun Bikin Duanwu

May 30, 2025
Koshin Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Inganta

Koshin Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Inganta

May 30, 2025
Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar

Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar

May 30, 2025
Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana

Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana

May 30, 2025
Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

May 30, 2025
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Hukumar Shiga Tsakani Ta Kasa Da Kasa A Hong Kong Na Kasar Sin

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Hukumar Shiga Tsakani Ta Kasa Da Kasa A Hong Kong Na Kasar Sin

May 30, 2025
Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

May 30, 2025
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Tattaunawa Ta Hudu Kan Musaya Da Koyi Da Juna A Tsakanin Al’ummomi Ta Fannin Wayewar Kansu

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Tattaunawa Ta Hudu Kan Musaya Da Koyi Da Juna A Tsakanin Al’ummomi Ta Fannin Wayewar Kansu

May 30, 2025
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas

May 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.