Ministan tsaron kasar Singapore Chan Chun Sing, ya fada a jiya Lahadi cewa, dole jama’ar kasar Sin ne za su iya tantance batun Taiwan ba wasu ba.
Da yake jawabi a zaman karshe na dandalin tattaunawa na Shangri-La karo na 22, Chan ya jaddada muhimmancin fahimtar yanayin tarihi na batun yankin Taiwan.
Ya ce, “Idan ba a kula da yadda za a tafiyar da warware wannan batun ba, jama’ar kasar Sin ne za su tantance abun da ya kamata a yi.”
Chan ya yi gargadi game da “juya akalar” bayanan da ake yi kan batun ta yadda ake masa kallon “rikici tsakanin dimokuradiyya da mulkin kama-karya,” ko kwatanta shi da na yanayin Ukraine. Yana mai cewar, jin ire-iren wannan yunkurin yana tsoratar da shi. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp