• English
  • Business News
Monday, October 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Wajen Sin Ya Yi Kira Da A Tsagaita Wuta A Gaza

by CGTN Hausa
2 years ago
Gaza

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya yi kira da a sassauta rikicin dake faruwa a tsakanin Isra’ila da Falasdinu, da ma ganin an tsagaita bude wuta a Gaza.

Wang, mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS, ya bayyana hakan ne, a yayin tattaunawa ta wayar tarho da mataimakin firaministan kasar Jordan kuma ministan harkokin wajen kasar Ayman Safadi jiya Alhamis.

  • Xi Jinping Ya Taya Murnar Gudanar Da Babban Taron Birane Masu Sada Zumunta Na Sin Da Amurka
  • Dakarun Tsaron Hadin Guiwa Sun Dakile Harin ‘Yan Ta’adda Da Cafke Mutum 2 A Kano

Wang ya ce, kasar Sin ta yi kakkausar suka ga hare-haren da ake kai wa sansanonin ’yan gudun hijira a zirin Gaza. Yana mai cewa, rayuwar al’ummar Falasdinu da Isra’ila duk muhimmancinsu daya, kuma bai kamata a rika nuna fuska biyu ba.

Wang ya jaddada cewa, kasar Sin tana goyon bayan muhimman shawarwarin da kasashen Larabawa suka gabatar game da tsagaita bude wuta, da wanzar da zaman lafiya. Ya ce, a matsayinta na shugabar karba-karba ta kwamitin sulhu na MDD na wannan watan, a shirye kasar Sin take ta ci gaba da yin cudanya da hadin gwiwa da dukkan bangarori, da yin duk mai yiwuwa wajen samar da daidaito a kwamitin sulhu, domin ganin an kwantar da hankula cikin gaggawa.

Ya ce da farko, ya kamata mu yi kokarin ganin an tsagaita bude wuta da kuma tabbatar da kai agajin jin kai ba tare da wani cikas ba. A halin da ake ciki kuma, ya kamata a hanzarta kiran taron zaman lafiya na kasa da kasa, don cimma sabon matsaya kan sake farfadowa da aiwatar da shawarwarin neman kafa kasashe biyu, da tsara takamaiman jadawalin lokaci da taswirar aiwatar da abubuwan da aka kai ga cimmawa.

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

A nasa bangare kuwa, Safadi ya godewa kasar Sin, bisa kokarinta na tabbatar da daidaito da adalci kan batun Falasdinu, da kuma goyon bayan kudurin da aka gabatar a taron gaggawa da babban zauren MDD ya kira. (Mai Fassarawa: Ibrahim Yaya)

 

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka
Daga Birnin Sin

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani
Daga Birnin Sin

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Next Post
Firaministan DR Congo Ya Kaddamar Da Cibiyar Bayanai Da Huawei Ya Gina

Firaministan DR Congo Ya Kaddamar Da Cibiyar Bayanai Da Huawei Ya Gina

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

October 27, 2025
Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

October 27, 2025
Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

October 27, 2025
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

October 27, 2025
Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.