ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Wajen Sin Ya Yi Kira Da A Tsagaita Wuta A Gaza

by CGTN Hausa
2 years ago
Gaza

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya yi kira da a sassauta rikicin dake faruwa a tsakanin Isra’ila da Falasdinu, da ma ganin an tsagaita bude wuta a Gaza.

Wang, mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS, ya bayyana hakan ne, a yayin tattaunawa ta wayar tarho da mataimakin firaministan kasar Jordan kuma ministan harkokin wajen kasar Ayman Safadi jiya Alhamis.

  • Xi Jinping Ya Taya Murnar Gudanar Da Babban Taron Birane Masu Sada Zumunta Na Sin Da Amurka
  • Dakarun Tsaron Hadin Guiwa Sun Dakile Harin ‘Yan Ta’adda Da Cafke Mutum 2 A Kano

Wang ya ce, kasar Sin ta yi kakkausar suka ga hare-haren da ake kai wa sansanonin ’yan gudun hijira a zirin Gaza. Yana mai cewa, rayuwar al’ummar Falasdinu da Isra’ila duk muhimmancinsu daya, kuma bai kamata a rika nuna fuska biyu ba.

ADVERTISEMENT

Wang ya jaddada cewa, kasar Sin tana goyon bayan muhimman shawarwarin da kasashen Larabawa suka gabatar game da tsagaita bude wuta, da wanzar da zaman lafiya. Ya ce, a matsayinta na shugabar karba-karba ta kwamitin sulhu na MDD na wannan watan, a shirye kasar Sin take ta ci gaba da yin cudanya da hadin gwiwa da dukkan bangarori, da yin duk mai yiwuwa wajen samar da daidaito a kwamitin sulhu, domin ganin an kwantar da hankula cikin gaggawa.

Ya ce da farko, ya kamata mu yi kokarin ganin an tsagaita bude wuta da kuma tabbatar da kai agajin jin kai ba tare da wani cikas ba. A halin da ake ciki kuma, ya kamata a hanzarta kiran taron zaman lafiya na kasa da kasa, don cimma sabon matsaya kan sake farfadowa da aiwatar da shawarwarin neman kafa kasashe biyu, da tsara takamaiman jadawalin lokaci da taswirar aiwatar da abubuwan da aka kai ga cimmawa.

LABARAI MASU NASABA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

A nasa bangare kuwa, Safadi ya godewa kasar Sin, bisa kokarinta na tabbatar da daidaito da adalci kan batun Falasdinu, da kuma goyon bayan kudurin da aka gabatar a taron gaggawa da babban zauren MDD ya kira. (Mai Fassarawa: Ibrahim Yaya)

 

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara
Daga Birnin Sin

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka
Daga Birnin Sin

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Next Post
Firaministan DR Congo Ya Kaddamar Da Cibiyar Bayanai Da Huawei Ya Gina

Firaministan DR Congo Ya Kaddamar Da Cibiyar Bayanai Da Huawei Ya Gina

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.