• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Yaɗa Labarai Ya Kafa Kwamitin Kare Haƙƙoƙin Naƙasassu

by Sulaiman
1 year ago
Labarai

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ba da umarnin kafa wani kwamiti mai mutum biyar da zai fito da tsarin aiki da Hukumar Naƙasassu ta Ƙasa domin wayar da kan jama’a game da ‘yanci da kuma damarmakin naƙasassu.

Ministan ya bayar da umarnin ne a Abuja a ranar Laraba a lokacin da ya karɓi baƙuncin Babban Sakataren Hukumar Nakasassu, Dakta James Lalu, a wata ziyarar ban-girma da ya kai ofishin sa.

  • Badakalar Fiye Da Biliyan 8: EFCC Ta Cafke Tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama, Hadi Sirika 
  • Ministan Harkokin Wajen Gabon Ya Yabawa Nasarorin Da Gabon Da Sin Suka Samu A Fannonin Sada Zumunta Da Hadin Gwiwa

Ya ce: “Daga yau, za mu kafa kwamitin da zai yi aiki kafaɗa da kafaɗa da ku don duba takamaiman buƙatun ku domin mu taimaka wajen ganin an cimma manufofin ku.”

Idris ya ƙara da cewa zai ba hukumar damar yin aiki da hukumomin yaɗa labarai da kayan aikin ma’aikatar sa domin kare haƙƙi da mutuncin naƙasassu da kare su daga wariya.

Ministan ya ce Shugaba Tinubu ya yi imani da haɗin kan jama’a, don haka ya jajirce wajen ba da ganuwa, karɓuwa, da alhaki ga naƙasassu a gwamnatin sa.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro

Ya ƙara da cewa, “Babu wani ɓangare na al’ummar Nijeriya da za a bari a baya a ƙarƙashin gwamnatin Tinubu.”

Ya yi alƙawarin jagorantar kai shawarwari ga gwamnonin jihohi game da tsarin doka na naƙasa a jihohin su.

A nasa jawabin, Dakta Lalu ya ce ya je ma’aikatar ne domin neman haɗin gwiwa domin wayar da kan jama’a kan haƙƙin naƙasassun.

Ya ce wasu sassan Dokar Naƙasa sun umurci masu ba da sabis da su samar da dama ta musamman ga naƙasassu a wurare kamar gine-ginen jama’a, sufuri, da wuraren kula da lafiya da sauran su ba tare da nuna wariya ba.

Dakta Lalu ya ce naƙasassu na da ɗimbin damarmaki waɗanda suka haɗa da fasahohi daban-daban, cancanta, da basirar da ake buƙata don cigaban tattalin arzikin ƙasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Radda
Labarai

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro

October 18, 2025
Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi
Manyan Labarai

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

October 18, 2025
Next Post
matsinn rayuwa

Duk Da Matsin Rayuwa: Hukumomi 7 Sun Kebe Wa Kansu Naira Biliyan 80.9 Na Jin Dadi

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Radda

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro

October 18, 2025
Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

October 18, 2025
IMF

Fitar Da Kudi Ta Haramtacciyar Hanya Na Kara Dagula Matsalar Tattalin Arziki – IMF

October 18, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci CBN Da Bankuna Kan Cire Wa Kwastomomi Kudi Ba Dalili

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
katsina

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

October 17, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

October 17, 2025
Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.