• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Alƙawarin Tallafawa Gidan Rediyon EFCC

by Sulaiman
1 year ago
Efcc

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi alƙawarin tallafa wa manufofin gidan rediyon Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa mai suna EFCC Radio.

Idris ya bayyana hakan ne a wurin taron ƙaddamar da gidan rediyon da ke kan lamba 97.3 a zangon FM wanda aka yi a hedikwatar hukumar a Jabi, Abuja a ranar Alhamis, 16 ga Mayu, 2024.

  • EFCC Za Ta Fara Amfani Da Fasahar Zamani Wajen Gano Masu Ɗaukar Nauyin Ta’addanci 
  • Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Zanta Da Takwaransa Na Tanzania

Ministan ya ce: “Ku tabbatar da cewa a matsayi na na Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, zan yi duk abin da zan iya don tallafa wa manufofin ku.”

Kafin yin wannan iƙirarin, ministan ya bayyana jin daɗin sa “da halartar wannan bikin ƙaddamar da sabuwar hanyar sadarwa a Nijeriya, wato EFCC Radio 97.3 FM.

“Dole ne in ce abin farin ciki ne sosai ganin ɗaya daga cikin manyan hukumomin tabbatar da doka da oda a ƙasar nan na ƙara faɗaɗa hanyoyin sadarwar jama’a da gudanar da ayyukan su ta hanyar kafa gidan rediyon FM.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

“A matsayin ta na hukumar da ke fuskantar jama’a, haƙiƙa yana da matuƙar muhimmanci Hukumar Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa (EFCC) ta tsara labaran da ke tattare da duk wani muhimmin yaƙi da ake yi da cin hanci da rashawa a ƙasar mu a tsanake da dabaru.”

Ya kuma yi alƙawarin cewa, “Tare da yin aiki ta hannun Hukumar Yaɗa Labarai ta Ƙasa (NBC), za mu kuma tabbatar da cewa mun ƙarfafa gwiwar sauran hukumomin gwamnati da abin ya shafa su yi haka, tare da bayar da gudunmawa wajen faɗakarwa da wayar da kan jama’a.”

A cewar ministan, “Ajandar mu ta biyu cikin 5 a Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai ita ce inganta manufofi da tsare-tsare na Gwamnatin Tarayya, kuma ina farin ciki da cewa a yanzu mun samu wannan sabuwar abokiyar hulɗa, EFCC Radio 97.3. FM, wacce za ta taimaka mana wajen cimma wannan manufa.

“Abu na farko na waccan ajandar mai ƙunshe da abubuwa biyar shi ne dawo da amana a harkokin sadarwar jama’a a Nijeriya.

“Ina so a kan haka, in umarci masu gudanarwa da ma’aikatan wannan sabuwar tashar, da su yi ƙoƙari su yi aiki a kowane lokaci bisa ƙa’idoji na aikin watsa labarai da aikin jarida.

“Ku ne abokan hulɗar mu masu ƙima yayin da muke neman sake ginawa da dawo da yardar al’ummar Nijeriya kan bayanan da ke fitowa daga Gwamnatin Tarayya.

“A kan haka, bari in sake taya Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Da Rashawa (EFCC) murna, kan wannan rawar da ta taka. Ina yi maku fatan alheri yayin da kuka fara aiki gaba ɗaya.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140
Labarai

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Majalisar Dattawa
Labarai

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa
Labarai

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Next Post
Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Da Su Zuba Jari Da Aiwatar Da Hada-hada A Kasar

Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Da Su Zuba Jari Da Aiwatar Da Hada-hada A Kasar

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.