• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Alƙawarin Tallafawa Gidan Rediyon EFCC

by Sulaiman
12 months ago
in Labarai
0
Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Alƙawarin Tallafawa Gidan Rediyon EFCC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi alƙawarin tallafa wa manufofin gidan rediyon Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa mai suna EFCC Radio.

Idris ya bayyana hakan ne a wurin taron ƙaddamar da gidan rediyon da ke kan lamba 97.3 a zangon FM wanda aka yi a hedikwatar hukumar a Jabi, Abuja a ranar Alhamis, 16 ga Mayu, 2024.

  • EFCC Za Ta Fara Amfani Da Fasahar Zamani Wajen Gano Masu Ɗaukar Nauyin Ta’addanci 
  • Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Zanta Da Takwaransa Na Tanzania

Ministan ya ce: “Ku tabbatar da cewa a matsayi na na Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, zan yi duk abin da zan iya don tallafa wa manufofin ku.”

Kafin yin wannan iƙirarin, ministan ya bayyana jin daɗin sa “da halartar wannan bikin ƙaddamar da sabuwar hanyar sadarwa a Nijeriya, wato EFCC Radio 97.3 FM.

“Dole ne in ce abin farin ciki ne sosai ganin ɗaya daga cikin manyan hukumomin tabbatar da doka da oda a ƙasar nan na ƙara faɗaɗa hanyoyin sadarwar jama’a da gudanar da ayyukan su ta hanyar kafa gidan rediyon FM.

Labarai Masu Nasaba

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

“A matsayin ta na hukumar da ke fuskantar jama’a, haƙiƙa yana da matuƙar muhimmanci Hukumar Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa (EFCC) ta tsara labaran da ke tattare da duk wani muhimmin yaƙi da ake yi da cin hanci da rashawa a ƙasar mu a tsanake da dabaru.”

Ya kuma yi alƙawarin cewa, “Tare da yin aiki ta hannun Hukumar Yaɗa Labarai ta Ƙasa (NBC), za mu kuma tabbatar da cewa mun ƙarfafa gwiwar sauran hukumomin gwamnati da abin ya shafa su yi haka, tare da bayar da gudunmawa wajen faɗakarwa da wayar da kan jama’a.”

A cewar ministan, “Ajandar mu ta biyu cikin 5 a Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai ita ce inganta manufofi da tsare-tsare na Gwamnatin Tarayya, kuma ina farin ciki da cewa a yanzu mun samu wannan sabuwar abokiyar hulɗa, EFCC Radio 97.3. FM, wacce za ta taimaka mana wajen cimma wannan manufa.

“Abu na farko na waccan ajandar mai ƙunshe da abubuwa biyar shi ne dawo da amana a harkokin sadarwar jama’a a Nijeriya.

“Ina so a kan haka, in umarci masu gudanarwa da ma’aikatan wannan sabuwar tashar, da su yi ƙoƙari su yi aiki a kowane lokaci bisa ƙa’idoji na aikin watsa labarai da aikin jarida.

“Ku ne abokan hulɗar mu masu ƙima yayin da muke neman sake ginawa da dawo da yardar al’ummar Nijeriya kan bayanan da ke fitowa daga Gwamnatin Tarayya.

“A kan haka, bari in sake taya Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Da Rashawa (EFCC) murna, kan wannan rawar da ta taka. Ina yi maku fatan alheri yayin da kuka fara aiki gaba ɗaya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlmundahanaCin Hanci Da RashawaEFCC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kisan Gambo Mai Faci A Katsina: Iyalansa Sun Bar Wa Allah, Cewar Hisba

Next Post

Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Da Su Zuba Jari Da Aiwatar Da Hada-hada A Kasar

Related

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi
Labarai

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

1 hour ago
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja
Labarai

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

4 hours ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

5 hours ago
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 
Labarai

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

5 hours ago
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

6 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

8 hours ago
Next Post
Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Da Su Zuba Jari Da Aiwatar Da Hada-hada A Kasar

Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Da Su Zuba Jari Da Aiwatar Da Hada-hada A Kasar

LABARAI MASU NASABA

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.