ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Alƙawarin Tallafawa Gidan Rediyon EFCC

by Sulaiman
2 years ago
Efcc

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi alƙawarin tallafa wa manufofin gidan rediyon Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa mai suna EFCC Radio.

Idris ya bayyana hakan ne a wurin taron ƙaddamar da gidan rediyon da ke kan lamba 97.3 a zangon FM wanda aka yi a hedikwatar hukumar a Jabi, Abuja a ranar Alhamis, 16 ga Mayu, 2024.

  • EFCC Za Ta Fara Amfani Da Fasahar Zamani Wajen Gano Masu Ɗaukar Nauyin Ta’addanci 
  • Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Zanta Da Takwaransa Na Tanzania

Ministan ya ce: “Ku tabbatar da cewa a matsayi na na Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, zan yi duk abin da zan iya don tallafa wa manufofin ku.”

ADVERTISEMENT

Kafin yin wannan iƙirarin, ministan ya bayyana jin daɗin sa “da halartar wannan bikin ƙaddamar da sabuwar hanyar sadarwa a Nijeriya, wato EFCC Radio 97.3 FM.

“Dole ne in ce abin farin ciki ne sosai ganin ɗaya daga cikin manyan hukumomin tabbatar da doka da oda a ƙasar nan na ƙara faɗaɗa hanyoyin sadarwar jama’a da gudanar da ayyukan su ta hanyar kafa gidan rediyon FM.

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

“A matsayin ta na hukumar da ke fuskantar jama’a, haƙiƙa yana da matuƙar muhimmanci Hukumar Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa (EFCC) ta tsara labaran da ke tattare da duk wani muhimmin yaƙi da ake yi da cin hanci da rashawa a ƙasar mu a tsanake da dabaru.”

Ya kuma yi alƙawarin cewa, “Tare da yin aiki ta hannun Hukumar Yaɗa Labarai ta Ƙasa (NBC), za mu kuma tabbatar da cewa mun ƙarfafa gwiwar sauran hukumomin gwamnati da abin ya shafa su yi haka, tare da bayar da gudunmawa wajen faɗakarwa da wayar da kan jama’a.”

A cewar ministan, “Ajandar mu ta biyu cikin 5 a Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai ita ce inganta manufofi da tsare-tsare na Gwamnatin Tarayya, kuma ina farin ciki da cewa a yanzu mun samu wannan sabuwar abokiyar hulɗa, EFCC Radio 97.3. FM, wacce za ta taimaka mana wajen cimma wannan manufa.

“Abu na farko na waccan ajandar mai ƙunshe da abubuwa biyar shi ne dawo da amana a harkokin sadarwar jama’a a Nijeriya.

“Ina so a kan haka, in umarci masu gudanarwa da ma’aikatan wannan sabuwar tashar, da su yi ƙoƙari su yi aiki a kowane lokaci bisa ƙa’idoji na aikin watsa labarai da aikin jarida.

“Ku ne abokan hulɗar mu masu ƙima yayin da muke neman sake ginawa da dawo da yardar al’ummar Nijeriya kan bayanan da ke fitowa daga Gwamnatin Tarayya.

“A kan haka, bari in sake taya Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Da Rashawa (EFCC) murna, kan wannan rawar da ta taka. Ina yi maku fatan alheri yayin da kuka fara aiki gaba ɗaya.”

Efcc
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Next Post
Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Da Su Zuba Jari Da Aiwatar Da Hada-hada A Kasar

Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Da Su Zuba Jari Da Aiwatar Da Hada-hada A Kasar

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.