• English
  • Business News
Friday, October 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Najeriya Sun Gana A Beijing

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
Sin

Memban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar, Wang Yi, ya yi shawarwari tare da ministan harkokin wajen Najeriya, Yusuf Maitama Tuggar, jiya Jumma’a a Beijing.

Wang Yi ya ce, Najeriya babbar kasa ce a Afirka dake taka muhimmiyar rawa a fannoni daban-daban, kuma tana da matukar muhimmanci a cikin harkokin diflomasiyyar kasar Sin, gami da mu’amalarta da kasashen Afirka. Ya ce raya dangantakar kasashen biyu da kyau, ya dace da muradun al’ummominsu baki daya, kuma zai kafa wani kyakkyawan misali ga raya dangantakar kasar Sin da kasashen Afirka. Haka kuma, kasar Sin na fatan kasashen biyu za su ci gaba da marawa juna baya, da neman cimma moriya tare, da kiyaye zaman adalci da daidaito, tare da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali, don neman ci gaba cikin hadin-gwiwa, da ciyar da dangantakar Sin da Najeriya, har ma da Afirka, zuwa sabon matsayi.

  • ASUU Ta Ƙalubalanci Naɗa Yan Siyasa A Matsayin Shugabannin Gudanarwar Jami’oin
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Ci Bashin Dala Miliyan 500 Don Gina Hanyoyin Karkara

A nasa bangaren, Yusuf Maitama Tuggar ya ce, Najeriya za ta ci gaba da yin tsayin daka kan manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya, kana, tana fatan inganta mu’amala da manyan jami’an gwamnatin kasar Sin, da zurfafa tuntubar juna, da kara fadada hadin-gwiwarsu. Ya ce Najeriya tana kuma fatan hada kai da kasar Sin, don ingiza hadin-gwiwar kasashe masu tasowa, da tsayawa ga ra’ayin bunkasuwar bangarori daban-daban a duniya, da tabbatar da zaman adalci da tsare gaskiya a duniya.

Har wa yau, jami’an biyu sun kuma halarci cikakken zama na farko na kwamitocin gwamnatocin Sin da Najeriya, wanda aka yi jiya Jumma’a a Beijing, inda suka saurari rahotannin da kwamitin bangarori daban-daban na kasashen biyu suka gabatar, ciki har da siyasa, da diflomasiyya, da al’adu, da yawon shakatawa, da tattalin arziki, da cinikayya, da sana’ar noma, da tsaro da sauransu, tare kuma da tsara shirye-shiryen hadin-gwiwar kasashen biyu a nan gaba.

Wang Yi ya bayyana cewa, kwamitin gwamnatocin kasashen Sin da Najeriya, ya kasance irinsa na farko da kasar Sin ta kafa tare da kasashen Afirka, kuma ya dace bangarorin biyu su kara fahimtar ayyukan da za su yi, da sanya muhimman ra’ayoyi iri daya da aka cimma tsakanin shugabannin kasashen biyu a gaban komai, da daukar matakai a zahirance don kara cimma nasarori.

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

Shi kuma minista Tuggar ya yaba sosai da nasarorin da aka cimma a zaman taron na wannan karo, inda ya ce, Najeriya tana fatan ci gaba da zurfafa fahimtar juna da kasar Sin, don cimma karin nasarori a hadin-gwiwarsu a fannoni daban-daban.

Bayan taron, bangarorin biyu sun fitar da sanarwa cikin hadin-gwiwa game da cikakken zamansu karo na farko. (Murtala Zhang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika
Daga Birnin Sin

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

October 16, 2025
Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

October 16, 2025
Gaza
Daga Birnin Sin

Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar?

October 16, 2025
Next Post
Amfanin Mangwaro Ga Mata Masu Juna Biyu

Amfanin Mangwaro Ga Mata Masu Juna Biyu

LABARAI MASU NASABA

Manzon Allah

Manzon Allah (SAW) Ne Ya Kafa Tushen Wayewar Kai A Duniya

October 17, 2025
An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai

Yadda ‘Yan Bindiga Ke Zafafa Hare-hare A Jihohin Arewa Maso Yamma

October 17, 2025
Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

Afuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka: Ta Bar Baya Da Ƙura

October 17, 2025
Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027

Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027

October 17, 2025
Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

October 16, 2025
NAWIA

Ranar Abinci Ta Duniya: NAWIA Ta Tallafawa Mata 114  Da Kayan Aikin Gona A Zamfara

October 16, 2025
Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

October 16, 2025
Gaza

Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar?

October 16, 2025
Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

October 16, 2025
Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.