• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mitocin Lantarki Miliyan 5.3 Na Fuskantar Barazanar Daina Aiki

Yadda Ake Fafutukar Magance Lamarin

by Sani Anwar
2 years ago
in Labarai
0
Lantarki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar daidaita al’amuran wutar lantarki ta kasa (NERC), ta ankarar da ‘yan Nijeriya; musamman masu amfani da mitocin wutar lantarki, dangane da fuskantar barazanar daina aiki a watan Nuwamban 2024.

Bayan ayyana barazanar da hukumar ta yi na daina aikin mitocin a shekara mai zuwa, sai ga wasu daga cikin kamfanoni masu kula da rabon wutar lantarkin (DisCos), sun ja hankalin masu amfanin da mitocin cewa, akwai yiwuwar daga nan zuwa karshen wannan shekara mitocin za su daina aiki kwata-kwata, ta yadda ko kudi ba za a iya sanya musu ba.

  • Wata Sabuwa: Gwamna Ya Kai Karar Shugaban Majalisa Gaban Tinubu Kan Nada Shugabancin Kwamiti Mai Gwabi

Kamar yadda LEADERSHIP ta rawaito, Hukumar daidaita al’amuran wutar lantarkin, ta shawarci kamfanonin masu kula da rabon wutar lantarki, da su gaggauta wayar da kan kwastomominsu wajen sake sabunta mitocinsu, domin ci gaba da aiki kamar yadda suka saba, idan kuma ba haka ba; za su fuskanci mummunan kalubale wajen sanya musu kudi daga nan zuwa shekara mai zuwa.

A wata sanarwa da hukumar kula da rabon wutar lantarkin ta fitar a shafinta na Twitter, ta bayyana sake sabunta mitocin a matsayin kyauta ba tare da biyan ko sisin kwabo ba, illa kawai dai masu amfani da mitocin za su ziyarci kamfanonin kula da rabon wutar, domin nuna musu yadda za su sake sabunta su.

“idan kana da mita, magana ce kawai ta yadda za ka sake sabunta ta; ta ci gaba da yin aiki. Daga watan Nuwamban 2024, akwai yiwuwar ba za ka sake iya sanya wa mitarka kudi ba. Sannan, sake sabunta tan abu ne mai matukar sauki kuma kyauta.”

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

Har ila yau, “Kamfanonin rabon wutar lantarkin, akwai wasu lambobi da za su bayar a matsayin mabudi, wadanda za a yi amfani da su don sake sabunta mitocin kuma kyauta ba tare da kowa ya biya ba,” a cewar hukumar daidaita al’amuran wutar lantarki din.

Bugu da kari, “sabunta mitarka, ba zai shafi kudin da ke cikin ta ba, ko kwabonka ba zai yi ciwon kai ba, sannan ba zai kuma sa mitar ta kara sauri ko gudu ba, dazarar kuma ka ga daya cikin biyun, sai ka garzaya domin yin korafi a a ofishinsu mafi kusa a gyara maka,” a cewar tasu.

Haka zalika, kamar yadda reshen Ikeja na kamfanin kula da rabon wutar lantarkin, karkashin hukumar daidaita al’amuran wutar lantarki ya bayyana, kafatanin mitocin wutar lantarki ta duniya ciki har da Nijeriya, na fuskantar barazanar tsayawa tare da daina aiki a 24 ga watan Nuwamban 2024, sannan duk wanda bai yi kokarin sake sabunta mitar tasa ba, yana cike da barazanar zama cikin duhu daga 1 ga watan Nuwamban 2023.

Kamfanin rabon wutar lantarkin ya ci gaba da bayyana cewa; tuni ya gama shiryawa tsaf domin tunkarar wannan matsala. Hakan kuwa, ta faru ne sakamakon hobbasar da wani kamfani mai kula da sarrafa mitoci a Nijeriya ya yi (MOJEC), domin tallafa wa kamfanonin rabon wutar lantarki a Nijeriya, domin sake sabunta mitoci don amfanin ‘yan kasa baki-daya, musamman masu amfani da ita.

Manajan Daraktan Kamfanin Mita na MOJEC, Madam Chantelle Abdul, ta sake tabbatar da tabbacin bayar da wa’adin na barazanar daina aikin mitoci a Nijeriya, daga watan Nuwamban 2024 ba 2023 da wasu ke shelantawa ba.

Ta kara da cewa, hukumar daidaita al’amuran wutar lantarki (NERC), ita ce ke da alhakin kula tare da baiwa kamfanonin rabon wutar lantarkin da kuma na masu sarrafa mitoci umarni, musamman a wannan gaba da ake fuskantar barazana na daina aikin wadannan mitoci.

A cewar tata, umarnin a halin yanzu ya hada da tabbatar da ganin sabbin mitocin da za a samar na dauke da tsarin sabunta mitar na 2024, ba kuma daga bisani a ce sai an sake sabunta su ba.

Sannan, ta kara jan hankalin kananan kamfanoni masu tasarrafi da mitoci, da su tabbatar sun sabunta su kafin su sayar wa masu amfani da su kafin 2024. “Da zarar kamfanonin rabon wutar lantarki (Discos), sun sabunta wadannan mitoci, wajibi ne su ma sauran kananan kamfanoni masu tasarrafi da mitocin su sabunta su kafin kai wa ga sayarwa da mutane.

Kamar yadda rahoto ya bayyana, kamfanonin rabon wutar lantarki, sun samar da akalla mitoci 171,107 ga kwastomominsu a watanni hudun farkon wannan shekara ta 2023.

Haka zalika, rahoton ya kara nuni da cewa, a cikin mutane miliyan 12.38 da suka yi rijista don neman mita, miliyan 5.36 ne kacal suka samu. “A 31 ga watan Mayun 2023, wadanda suka nemi mita sun kai miliyan 12,378,243, amma miliyan 5,360,434 ne kadai sukaa samu.

A farkon wannan shekara, Gwamnatin Tarayya ta sha alwashin samar da mitoci kimanin miliyan shida a duk fadin Nijeriya, a watanni hudun farko da na tsakiyar shekarar, domin sake rage yawan wadanda ba sa amfani da mitar a fadin kasar.

An bayyana hakan ne a watan Disambar 2022, a yayin sake tantance ayyuka tare da dora ayyukan da ma’aikatar kula da wutar lantarki ta kasa ta yi karkashin kulawar wannan gwamnati a sikeli.

Har ila yau, ma’aikatar kula da wutar lantarkin ta kasa, ta bayyana nasarar da ta samu na samar da akalla mitoci miliyan daya, a shirnta na kokarin wadata kasa da mitoci.

Haka zalika, Babban Bankin Nijeriya na Kasa tare da Hukumar daidaita al’amuran wutar lantarki, su ne kinshikai wajen tabbatar da nasara, tsarawa da kuma tabbatar da shirin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: LantarkiTCN
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hasashe Kan Yadda Wasan Ac Milan Da Inter Milan Zai Kaya

Next Post

Gwamnatin Jihar Enugu Ta Haramta Hakar Ma’adinai Ta Haramtacciyar Hanya

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

5 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

6 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

15 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

17 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

18 hours ago
Next Post
Gwamnatin Jihar Enugu Ta Haramta Hakar Ma’adinai Ta Haramtacciyar Hanya

Gwamnatin Jihar Enugu Ta Haramta Hakar Ma'adinai Ta Haramtacciyar Hanya

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.