ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wata Sabuwa: Gwamna Ya Kai Karar Shugaban Majalisa Gaban Tinubu Kan Nada Shugabancin Kwamiti Mai Gwabi

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Tinubu

Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma ya kai karar shugaban majalisar wakilai, Tajudeen Abbas gaban Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu bisa daukaka dan majalisar jiharsa, Ikenga Imo Ugochinyere wajen ba shi kwamiti mai gwabi a cikin gwamnatin jam’iyyar APC. 

Uzodinma ya bayyana rashin jin dadinsa ga Abbas wajen martaba Ugochinyere, wanda ya kasance dan majalisa a karkashin tutur jam’iyyar PDP, na danka masa shugabancin kwamitin man fetur (da aka tace).

  • Remi Tinubu Ta Bada Tallafin Naira Miliyan N500 Ga Iyalai 500 Da Rikici Ya Shafa A Jihar Filato

An bayyana cewa Uzodinma wanda ya kasance shugaban kungiyar gwamnonin APC ya kalubalance nadi bokin hamayyarsa shugaban kwamitin majalisa mai gwabi tun loacin da aka sanar da nadin.

ADVERTISEMENT

LEADERSHIP ta ruwaito cewa shugaban majalisar wakilai Abbas ya fusata Uzo-dinma wanda yake ganin cewa wannan nadin zai bai wa Ugochinyere shahara a cikin harkokin siyasa.

Bayan haka kuma, an bayyana cewa gwamnan ya dauki nadin dan majalisar a matsayin shugaban kwamitin mai gwabi za sa dan adawa ya kara karfi a siyasance, wanda hakan cin mutunci ne a matsayinsa na gwamnan jihar kuma shugaban kungiyar gwamnonin APC.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Wata majiya da ke kusa da gwamnan ta bayyana cewa, lallai gwamnan ya yi matukar fusata da nadin Ugochinyere wanda hakan zai taba kimarsa a matsayinsa na gwamnan Jihar Imo.

A cewar wata majiyar, Uzodinma ya damu sosai na nadin Ugochinyere shugabancin kwamitin mai gwabi a zauren majalisar wakilai na tarayya, wanda hakan zai kara wa ‘yan adawa karfi a cikin harkokin siyasa.

Duk da dai kotun sauraron kararrakin zabe da ke zamanta a Jihar Nasarawa ta soke zaben Ugochinyere, dan majalisar ya daukaka kara na kalubalantar hukuncin a kotun daukaka kara.

Ugochinyere zai ci gaba da zama dan majalisar wakilai har sai kotun daukaka kara ta zantar da hukunci.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa Uzodinma ya yi kokarin shawo kan Abbas kan ya janye nadin.

An samu rahoton da ke cewa shugaban majalisar wakilan ya yi watsi da bukatar gwamnan.

LEADERSHIP ta kuma kara da cewa tuni Uzodinma ya kai karar Abbas gaban Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu kan wannan nadin.

Har ila yau, a nasa martanin, Ugochinyere ya bukaci Uzodinma ya cire Abbas daga ciki siyasar Jihar Imo.

A wata tattaunawa ta wayar tarho, dan majalisar da ke cikin rudani ya bayyana cewa ba sai ya bukaci goyon bayan Abbas ba wajen murkushe Uzodinma a zabe mai zuwa a jihar.

Ya siffanta Uzodimma a matsayin karamin kwaro a siyasa. Ya ce, “Za mu mur-kushe Uzodinma a zaben gwamna a watan Nuwamba kamar yadda muka yi a zaben watan Mayu.”

Tinubu
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili

Martanin Obaseki Ga Wike Kan Kiran Dakatar Da Atiku Daga PDP…

LABARAI MASU NASABA

NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026
Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.