ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wata Sabuwa: Gwamna Ya Kai Karar Shugaban Majalisa Gaban Tinubu Kan Nada Shugabancin Kwamiti Mai Gwabi

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Tinubu

Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma ya kai karar shugaban majalisar wakilai, Tajudeen Abbas gaban Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu bisa daukaka dan majalisar jiharsa, Ikenga Imo Ugochinyere wajen ba shi kwamiti mai gwabi a cikin gwamnatin jam’iyyar APC. 

Uzodinma ya bayyana rashin jin dadinsa ga Abbas wajen martaba Ugochinyere, wanda ya kasance dan majalisa a karkashin tutur jam’iyyar PDP, na danka masa shugabancin kwamitin man fetur (da aka tace).

  • Remi Tinubu Ta Bada Tallafin Naira Miliyan N500 Ga Iyalai 500 Da Rikici Ya Shafa A Jihar Filato

An bayyana cewa Uzodinma wanda ya kasance shugaban kungiyar gwamnonin APC ya kalubalance nadi bokin hamayyarsa shugaban kwamitin majalisa mai gwabi tun loacin da aka sanar da nadin.

ADVERTISEMENT

LEADERSHIP ta ruwaito cewa shugaban majalisar wakilai Abbas ya fusata Uzo-dinma wanda yake ganin cewa wannan nadin zai bai wa Ugochinyere shahara a cikin harkokin siyasa.

Bayan haka kuma, an bayyana cewa gwamnan ya dauki nadin dan majalisar a matsayin shugaban kwamitin mai gwabi za sa dan adawa ya kara karfi a siyasance, wanda hakan cin mutunci ne a matsayinsa na gwamnan jihar kuma shugaban kungiyar gwamnonin APC.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

Wata majiya da ke kusa da gwamnan ta bayyana cewa, lallai gwamnan ya yi matukar fusata da nadin Ugochinyere wanda hakan zai taba kimarsa a matsayinsa na gwamnan Jihar Imo.

A cewar wata majiyar, Uzodinma ya damu sosai na nadin Ugochinyere shugabancin kwamitin mai gwabi a zauren majalisar wakilai na tarayya, wanda hakan zai kara wa ‘yan adawa karfi a cikin harkokin siyasa.

Duk da dai kotun sauraron kararrakin zabe da ke zamanta a Jihar Nasarawa ta soke zaben Ugochinyere, dan majalisar ya daukaka kara na kalubalantar hukuncin a kotun daukaka kara.

Ugochinyere zai ci gaba da zama dan majalisar wakilai har sai kotun daukaka kara ta zantar da hukunci.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa Uzodinma ya yi kokarin shawo kan Abbas kan ya janye nadin.

An samu rahoton da ke cewa shugaban majalisar wakilan ya yi watsi da bukatar gwamnan.

LEADERSHIP ta kuma kara da cewa tuni Uzodinma ya kai karar Abbas gaban Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu kan wannan nadin.

Har ila yau, a nasa martanin, Ugochinyere ya bukaci Uzodinma ya cire Abbas daga ciki siyasar Jihar Imo.

A wata tattaunawa ta wayar tarho, dan majalisar da ke cikin rudani ya bayyana cewa ba sai ya bukaci goyon bayan Abbas ba wajen murkushe Uzodinma a zabe mai zuwa a jihar.

Ya siffanta Uzodimma a matsayin karamin kwaro a siyasa. Ya ce, “Za mu mur-kushe Uzodinma a zaben gwamna a watan Nuwamba kamar yadda muka yi a zaben watan Mayu.”

Tinubu
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Tinubu
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili

Martanin Obaseki Ga Wike Kan Kiran Dakatar Da Atiku Daga PDP…

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.