• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

More Ci Gaba Tare Wata Babbar Manufa Ce Ta Kasar Sin 

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
More Ci Gaba Tare Wata Babbar Manufa Ce Ta Kasar Sin 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanakin baya, wasu dalibai ’yan Najeriya 65 sun kammala karatu a kasar Sin, sun kuma koma gida. Bisa tallafin da wani kamfanin kasar Sin ya ba su, wadannan dalibai sun gama karatun ilimin injiniyan gini, da fannin jigilar kayayyaki a jami’o’in kasar Sin, inda suka samu digiri na farko ko na biyu. Galibinsu za su fara aiki a kamfanonin kasar Sin dake Najeriya, inda za su samar da gudunmowa ga aikin raya masana’antu masu alaka da zirga-zirgar jiragen kasa a kasarsu ta Najeriya.

Batun nan ya nuna sahihancin kasar Sin a fannin taimakawa Najeriya wajen samun ci gaba. Ban da daukar nauyin gina layin dogo na Abuja-Kano, da na Lagos-Ibadan, da layin jirgin kasa a birnin Abuja, da dai sauran ingantattun kayayyakin more rayuwa a Najeriya, kasar Sin ta kuma ba da taimako a fannin horar da kwararrun da suka san yadda ake sarrafawa da kulawa da kayayyakin. Ban da haka kuma, kasar ta mika wa matasan Najeriya damammaki na samun ilimi, da guraben aikin yi, da na cimma manyan burikan da suka sanya a gaba.

  • Sin Da Amurka Na Da Bukatar Karfafa Hadin Gwiwa, In Ji Firaministan Kasar Sin

Hakika, idan mun yi tsokaci kan manufofin kasar Sin na hulda da sauran kasashe, za mu ga yadda “more ci gaba tare” ya kasance wani muhimmin bangare a cikinsu. Cikin “shawarar neman samun ci gaba a duk duniya” wadda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar, ya ambaci fannonin da suka hada da taimakawa sauran kasashe masu tasowa samun ci gaban tattalin arziki, da kyautata zaman rayuwar jama’arsu, da hadin kai da sauran kasashe a kokarin rage talauci, da tabbatar da samar da isashen abinci, da samar da jarin da ake bukata don neman ci gaba, da raya kasa ba tare da gurbata muhalli ba, da raya masana’antu, da dai makamantansu.

Ban da haka kuma, kasar Sin ta daukaka tunanin “Kyan alkawari cikawa”. Tun da ta ba da shawarar “more ci gaba tare”, to, dole ne ta yi kokarin aiwatar da manufar. Game da haka, za a iya duba abubuwan dake faruwa a dab da mu, wadanda suka kasance misalai ga yadda hadin gwiwa tare da kasar Sin ke haifar da ci gaba ga kasashen Afirka:

A kasar Mauritius dake gabashin Afirka, wani kamfanin kasar Sin ya gina wata madatsar ruwa a dab da birnin Port Louis na kasar, wadda ta kawo karshen matsalar karancin ruwa da birnin ke fuskanta, ta yadda mazauna wurin suke iya samun ruwan famfo. Wannan shi ne misalin yadda ake samun ingantuwar zaman rayuwar jama’a.

Labarai Masu Nasaba

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

A kasar Kenya kuma, layin dogon da aka gina a tsakanin Mombasa da Nairobi, ya rage lokacin zirga-zirga a tsakanin biranen daga sa’o’i 10 zuwa sa’o’i 4. Ya kuma sanya ‘yan kasuwan kasar murna sosai, domin kudin da suke kashewa wajen jigilar kaya ya ragu da kashi 79%. Hakan misali ne na kyautatuwar muhallin ciniki, da aka samu ta hanyar hadin gwiwa da kasar Sin.

Haka zalika, cikin shekaru fiye da goma da suka gabata, ta hanyar gudanar da kwas na gajeren lokaci, kasar Sin ta taimaki kasashen Afirka wajen horar da mutane fiye da dubu 300, wadanda suka zama kwararru a fannonin aikin gona, da kula da itatuwa, da kare muhalli, da dai sauransu. Wannan ya nuna yadda kasar Sin take taimakawa kasashen Afirka wajen samun karfin raya tattalin arziki ta hanyar dogaro da kai.

Ko a nahiyar Afirka, ko a sauran wurare da kusurwoyin duniya, za a iya ganin dimbin misalai iri daya da wadanda muka ambata. Sai dai me ya sa kasar Sin ke son yayata ra’ayin “more ci gaba tare” a duniya?

Dalilin da ya sa haka shi ne al’adun gargajiyar kasar. Kaka da kakanin Sinawa, musamman ma wasu shahararrun malamai masu ilimi sun taba bayyana cewa, “ Duk wani abun da ba ka so, kar ka yi shi kan sauran mutane”, kana “ Mutum mai kirki ya fi dora muhimmanci kan kare adalci maimakon moriyar kai”. Ban da haka kuma, sun ce, “A yayin da kake kula da tsoffi da yara dake gidanka, kar ka manta da taimakon tsoffi da yara na gidajen sauran mutane.” Wannan tunani da al’adu mai alaka da shi sun sa Sinawa darajanta yanayin daidato, da adalci, da more alheri tare, gami da samun jituwa.

Sa’an nan wannan nau’in al’adu na gargajiya ya tabbatar da cewa, kasar Sin ba za ta mai da moriyar kanta a gaban ta sauran kasashe ba, kuma ba za ta taba neman yin babakere a duniya ba. Bayan da kasar ta samu nasarar raya kanta daga wata kasa mai talauci zuwa kasa mai karfin tattalin arziki tattalin arziki ta biyu a duniya, tare da samun dimbin fasahohi a fannin neman ci gaba, kasar na kuma son raba fasahohinta da sauran kasashe, da hadin gwiwa da su don neman damar samun ci gaban tattalin arziki na bai daya. Saboda bisa tunanin Sinawa, duniya ba za ta zama mai kyau ba, har sai an tabbatar da dadaito, da zaman lafiya, da more ci gaba, da wayewar kai a cikinta. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jami’in Ghana: Ci Gaban Sin A Fannin Noma Da Yaki Da Fatara Na Karfafa Gwiwar Sauran Kasashe Masu Tasowa

Next Post

Tinubu Ya Nemi Majalisa Ta Tabbatar Da Nadin Sabbin Hafsoshin Tsaron Nijeriya

Related

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila
Daga Birnin Sin

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

55 minutes ago
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

20 hours ago
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

21 hours ago
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

22 hours ago
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa
Daga Birnin Sin

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

23 hours ago
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata
Daga Birnin Sin

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

1 day ago
Next Post
Kasar Sin

Tinubu Ya Nemi Majalisa Ta Tabbatar Da Nadin Sabbin Hafsoshin Tsaron Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.