ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

More Ci Gaba Tare Wata Babbar Manufa Ce Ta Kasar Sin 

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

Kwanakin baya, wasu dalibai ’yan Najeriya 65 sun kammala karatu a kasar Sin, sun kuma koma gida. Bisa tallafin da wani kamfanin kasar Sin ya ba su, wadannan dalibai sun gama karatun ilimin injiniyan gini, da fannin jigilar kayayyaki a jami’o’in kasar Sin, inda suka samu digiri na farko ko na biyu. Galibinsu za su fara aiki a kamfanonin kasar Sin dake Najeriya, inda za su samar da gudunmowa ga aikin raya masana’antu masu alaka da zirga-zirgar jiragen kasa a kasarsu ta Najeriya.

Batun nan ya nuna sahihancin kasar Sin a fannin taimakawa Najeriya wajen samun ci gaba. Ban da daukar nauyin gina layin dogo na Abuja-Kano, da na Lagos-Ibadan, da layin jirgin kasa a birnin Abuja, da dai sauran ingantattun kayayyakin more rayuwa a Najeriya, kasar Sin ta kuma ba da taimako a fannin horar da kwararrun da suka san yadda ake sarrafawa da kulawa da kayayyakin. Ban da haka kuma, kasar ta mika wa matasan Najeriya damammaki na samun ilimi, da guraben aikin yi, da na cimma manyan burikan da suka sanya a gaba.

  • Sin Da Amurka Na Da Bukatar Karfafa Hadin Gwiwa, In Ji Firaministan Kasar Sin

Hakika, idan mun yi tsokaci kan manufofin kasar Sin na hulda da sauran kasashe, za mu ga yadda “more ci gaba tare” ya kasance wani muhimmin bangare a cikinsu. Cikin “shawarar neman samun ci gaba a duk duniya” wadda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar, ya ambaci fannonin da suka hada da taimakawa sauran kasashe masu tasowa samun ci gaban tattalin arziki, da kyautata zaman rayuwar jama’arsu, da hadin kai da sauran kasashe a kokarin rage talauci, da tabbatar da samar da isashen abinci, da samar da jarin da ake bukata don neman ci gaba, da raya kasa ba tare da gurbata muhalli ba, da raya masana’antu, da dai makamantansu.

ADVERTISEMENT

Ban da haka kuma, kasar Sin ta daukaka tunanin “Kyan alkawari cikawa”. Tun da ta ba da shawarar “more ci gaba tare”, to, dole ne ta yi kokarin aiwatar da manufar. Game da haka, za a iya duba abubuwan dake faruwa a dab da mu, wadanda suka kasance misalai ga yadda hadin gwiwa tare da kasar Sin ke haifar da ci gaba ga kasashen Afirka:

A kasar Mauritius dake gabashin Afirka, wani kamfanin kasar Sin ya gina wata madatsar ruwa a dab da birnin Port Louis na kasar, wadda ta kawo karshen matsalar karancin ruwa da birnin ke fuskanta, ta yadda mazauna wurin suke iya samun ruwan famfo. Wannan shi ne misalin yadda ake samun ingantuwar zaman rayuwar jama’a.

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

A kasar Kenya kuma, layin dogon da aka gina a tsakanin Mombasa da Nairobi, ya rage lokacin zirga-zirga a tsakanin biranen daga sa’o’i 10 zuwa sa’o’i 4. Ya kuma sanya ‘yan kasuwan kasar murna sosai, domin kudin da suke kashewa wajen jigilar kaya ya ragu da kashi 79%. Hakan misali ne na kyautatuwar muhallin ciniki, da aka samu ta hanyar hadin gwiwa da kasar Sin.

Haka zalika, cikin shekaru fiye da goma da suka gabata, ta hanyar gudanar da kwas na gajeren lokaci, kasar Sin ta taimaki kasashen Afirka wajen horar da mutane fiye da dubu 300, wadanda suka zama kwararru a fannonin aikin gona, da kula da itatuwa, da kare muhalli, da dai sauransu. Wannan ya nuna yadda kasar Sin take taimakawa kasashen Afirka wajen samun karfin raya tattalin arziki ta hanyar dogaro da kai.

Ko a nahiyar Afirka, ko a sauran wurare da kusurwoyin duniya, za a iya ganin dimbin misalai iri daya da wadanda muka ambata. Sai dai me ya sa kasar Sin ke son yayata ra’ayin “more ci gaba tare” a duniya?

Dalilin da ya sa haka shi ne al’adun gargajiyar kasar. Kaka da kakanin Sinawa, musamman ma wasu shahararrun malamai masu ilimi sun taba bayyana cewa, “ Duk wani abun da ba ka so, kar ka yi shi kan sauran mutane”, kana “ Mutum mai kirki ya fi dora muhimmanci kan kare adalci maimakon moriyar kai”. Ban da haka kuma, sun ce, “A yayin da kake kula da tsoffi da yara dake gidanka, kar ka manta da taimakon tsoffi da yara na gidajen sauran mutane.” Wannan tunani da al’adu mai alaka da shi sun sa Sinawa darajanta yanayin daidato, da adalci, da more alheri tare, gami da samun jituwa.

Sa’an nan wannan nau’in al’adu na gargajiya ya tabbatar da cewa, kasar Sin ba za ta mai da moriyar kanta a gaban ta sauran kasashe ba, kuma ba za ta taba neman yin babakere a duniya ba. Bayan da kasar ta samu nasarar raya kanta daga wata kasa mai talauci zuwa kasa mai karfin tattalin arziki tattalin arziki ta biyu a duniya, tare da samun dimbin fasahohi a fannin neman ci gaba, kasar na kuma son raba fasahohinta da sauran kasashe, da hadin gwiwa da su don neman damar samun ci gaban tattalin arziki na bai daya. Saboda bisa tunanin Sinawa, duniya ba za ta zama mai kyau ba, har sai an tabbatar da dadaito, da zaman lafiya, da more ci gaba, da wayewar kai a cikinta. (Bello Wang)

Kasar Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
Daga Birnin Sin

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Next Post
Kasar Sin

Tinubu Ya Nemi Majalisa Ta Tabbatar Da Nadin Sabbin Hafsoshin Tsaron Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.