• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mu’amala A Tsakanin Sin Da Manyan Kasashen Duniya A Shekarar 2022

by CMG Hausa
3 years ago
Sin

A cikin shekarar 2022, shugabannin Sin da Rasha sun gana a birnin Beijing na kasar Sin a yayin gasar wasannin Olympics ta lokacin hunturu ta shekarar 2022, shugabannin Sin da Amurka sun gana a tsibirin Bali, kana akwai ganawa tsakanin shugaban Sin da shugabannin kasashen Faransa, da Jamus da sauransu, wadanda suka shaida cewa, Sin ta sauke nauyin dake wuyanta a matsayinta na babbar kasa.

A karkashin jagorancin shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na kasar Rasha Vladimir Putin, a cikin shekarar da ta gabata, Sin da Rasha sun nuna goyon baya ga juna wajen kiyaye muhimman moriyarsu, da kara yin imani da juna kan harkokin siyasa da manyan tsare-tsare, da kuma inganta hadin gwiwar dake tsakanin kasashen biyu. Dangantaka tsakanin Sin da Rasha bisa tushen nuna daidaito da nuna adawa da kafa wani gungun kawance da rashin nuna kiyayya da juna da kin amincewa ga wani bangare na daban ta kara samun ingantuwa.

Game da dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka, a yayin ganawar shugabannin Sin da Amurka a tsibirin Bali, shugaba Xi Jinping ya yi bayani a fili game da hakikanin dangantakar Sin da Amurka, da bayyana abin da Sin take adawa, inda ya jaddada cewa, ya kamata a yi watsi da akidar samun nasara daga faduwar wani bangare. Haka kuma ya kamata a rika yin shawarwari da samun moriyar juna, bisa ka’idojin girmama juna da zama tare cikin lumana da hadin gwiwa don samun moriyar juna, an sa kaimi ga maido da raya dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka yadda ya kamata.

A shekarar 2022, shugaba Xi Jinping ya buga waya ko ganawa fiye da 20 tare da shugabannin kasashen Turai. An kuma samu karuwar zuba jari da cinikayya a tsakanin Sin da Turai, da fara aiwatar da manyan ayyukan dake shafar bangarorin biyu, wannan ya shaida cewa, Sin da Turai abokan hulda ne ba abokan gaba ba, sun kuma samu damammaki maimakon kawo barazana ga juna .

Idan har ana fatan duniya ta gyaru, wajibi ne manyan kasashe su kasance abin misali da daukar nauyin dake bisa wuyansu yadda ya kamata. Domin yadda irin wadannan manyan kasashe ke mu’amula da juna, yana da tasiri sosai kan makomar daukacin bil-Adama. (Zainab)

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

November 7, 2025
Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta

November 7, 2025
Xi Jinping Ya Taya Paul Biya Murnar Tazarce a Kamaru
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Taya Paul Biya Murnar Tazarce a Kamaru

November 7, 2025
Next Post
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Dangane Da Yunkurinta Na Toshe Kofofin Wasu Kasashe Na Samun Ci Gaba

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Dangane Da Yunkurinta Na Toshe Kofofin Wasu Kasashe Na Samun Ci Gaba

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

November 7, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

November 7, 2025
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

November 7, 2025
Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

November 7, 2025
Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)

Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)

November 7, 2025
Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

November 7, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya

November 7, 2025
An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

November 7, 2025
Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

November 7, 2025
Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta

Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.