• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mu’amala A Tsakanin Sin Da Manyan Kasashen Duniya A Shekarar 2022

by CMG Hausa
3 years ago
Sin

A cikin shekarar 2022, shugabannin Sin da Rasha sun gana a birnin Beijing na kasar Sin a yayin gasar wasannin Olympics ta lokacin hunturu ta shekarar 2022, shugabannin Sin da Amurka sun gana a tsibirin Bali, kana akwai ganawa tsakanin shugaban Sin da shugabannin kasashen Faransa, da Jamus da sauransu, wadanda suka shaida cewa, Sin ta sauke nauyin dake wuyanta a matsayinta na babbar kasa.

A karkashin jagorancin shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na kasar Rasha Vladimir Putin, a cikin shekarar da ta gabata, Sin da Rasha sun nuna goyon baya ga juna wajen kiyaye muhimman moriyarsu, da kara yin imani da juna kan harkokin siyasa da manyan tsare-tsare, da kuma inganta hadin gwiwar dake tsakanin kasashen biyu. Dangantaka tsakanin Sin da Rasha bisa tushen nuna daidaito da nuna adawa da kafa wani gungun kawance da rashin nuna kiyayya da juna da kin amincewa ga wani bangare na daban ta kara samun ingantuwa.

Game da dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka, a yayin ganawar shugabannin Sin da Amurka a tsibirin Bali, shugaba Xi Jinping ya yi bayani a fili game da hakikanin dangantakar Sin da Amurka, da bayyana abin da Sin take adawa, inda ya jaddada cewa, ya kamata a yi watsi da akidar samun nasara daga faduwar wani bangare. Haka kuma ya kamata a rika yin shawarwari da samun moriyar juna, bisa ka’idojin girmama juna da zama tare cikin lumana da hadin gwiwa don samun moriyar juna, an sa kaimi ga maido da raya dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka yadda ya kamata.

A shekarar 2022, shugaba Xi Jinping ya buga waya ko ganawa fiye da 20 tare da shugabannin kasashen Turai. An kuma samu karuwar zuba jari da cinikayya a tsakanin Sin da Turai, da fara aiwatar da manyan ayyukan dake shafar bangarorin biyu, wannan ya shaida cewa, Sin da Turai abokan hulda ne ba abokan gaba ba, sun kuma samu damammaki maimakon kawo barazana ga juna .

Idan har ana fatan duniya ta gyaru, wajibi ne manyan kasashe su kasance abin misali da daukar nauyin dake bisa wuyansu yadda ya kamata. Domin yadda irin wadannan manyan kasashe ke mu’amula da juna, yana da tasiri sosai kan makomar daukacin bil-Adama. (Zainab)

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

October 17, 2025
An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

October 17, 2025
Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki
Daga Birnin Sin

Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

October 17, 2025
Next Post
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Dangane Da Yunkurinta Na Toshe Kofofin Wasu Kasashe Na Samun Ci Gaba

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Dangane Da Yunkurinta Na Toshe Kofofin Wasu Kasashe Na Samun Ci Gaba

LABARAI MASU NASABA

Radda

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro

October 18, 2025
Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

October 18, 2025
IMF

Fitar Da Kudi Ta Haramtacciyar Hanya Na Kara Dagula Matsalar Tattalin Arziki – IMF

October 18, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci CBN Da Bankuna Kan Cire Wa Kwastomomi Kudi Ba Dalili

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
katsina

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

October 17, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

October 17, 2025
Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

October 17, 2025
Abduljabbar

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.