ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mu’amala A Tsakanin Sin Da Manyan Kasashen Duniya A Shekarar 2022

by CMG Hausa
3 years ago
Sin

A cikin shekarar 2022, shugabannin Sin da Rasha sun gana a birnin Beijing na kasar Sin a yayin gasar wasannin Olympics ta lokacin hunturu ta shekarar 2022, shugabannin Sin da Amurka sun gana a tsibirin Bali, kana akwai ganawa tsakanin shugaban Sin da shugabannin kasashen Faransa, da Jamus da sauransu, wadanda suka shaida cewa, Sin ta sauke nauyin dake wuyanta a matsayinta na babbar kasa.

A karkashin jagorancin shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na kasar Rasha Vladimir Putin, a cikin shekarar da ta gabata, Sin da Rasha sun nuna goyon baya ga juna wajen kiyaye muhimman moriyarsu, da kara yin imani da juna kan harkokin siyasa da manyan tsare-tsare, da kuma inganta hadin gwiwar dake tsakanin kasashen biyu. Dangantaka tsakanin Sin da Rasha bisa tushen nuna daidaito da nuna adawa da kafa wani gungun kawance da rashin nuna kiyayya da juna da kin amincewa ga wani bangare na daban ta kara samun ingantuwa.

Game da dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka, a yayin ganawar shugabannin Sin da Amurka a tsibirin Bali, shugaba Xi Jinping ya yi bayani a fili game da hakikanin dangantakar Sin da Amurka, da bayyana abin da Sin take adawa, inda ya jaddada cewa, ya kamata a yi watsi da akidar samun nasara daga faduwar wani bangare. Haka kuma ya kamata a rika yin shawarwari da samun moriyar juna, bisa ka’idojin girmama juna da zama tare cikin lumana da hadin gwiwa don samun moriyar juna, an sa kaimi ga maido da raya dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka yadda ya kamata.

ADVERTISEMENT

A shekarar 2022, shugaba Xi Jinping ya buga waya ko ganawa fiye da 20 tare da shugabannin kasashen Turai. An kuma samu karuwar zuba jari da cinikayya a tsakanin Sin da Turai, da fara aiwatar da manyan ayyukan dake shafar bangarorin biyu, wannan ya shaida cewa, Sin da Turai abokan hulda ne ba abokan gaba ba, sun kuma samu damammaki maimakon kawo barazana ga juna .

Idan har ana fatan duniya ta gyaru, wajibi ne manyan kasashe su kasance abin misali da daukar nauyin dake bisa wuyansu yadda ya kamata. Domin yadda irin wadannan manyan kasashe ke mu’amula da juna, yana da tasiri sosai kan makomar daukacin bil-Adama. (Zainab)

LABARAI MASU NASABA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
Daga Birnin Sin

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines
Daga Birnin Sin

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Dangane Da Yunkurinta Na Toshe Kofofin Wasu Kasashe Na Samun Ci Gaba

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Dangane Da Yunkurinta Na Toshe Kofofin Wasu Kasashe Na Samun Ci Gaba

LABARAI MASU NASABA

Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

June 13, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

June 13, 2026
Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.