• English
  • Business News
Saturday, May 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muhammad Salah: Gwarzon Afirka A Firimiyar Ingila

by Abba Ibrahim Wada and Sulaiman
4 months ago
in Wasanni
0
Muhammad Salah: Gwarzon Afirka A Firimiyar Ingila
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kawo yanzu dai babu wani dan wasa da yake nuna bajinta daga nahiyar Afirka a gasar Firimiya kamar dan wasa Muhammad Salah na kasar Masar wanda yake buga wasa a kungiyar kwallon kafa ta Liverpool domin kusan duk mako sai ya nuna bajinta. Dan wasan gaban na Liverpool ya zura kwallo biyu a wasan da kungiyar ta lallasa Tottenham da ci shida da uku kuma da wannan nasarar ce Salah ya haura dan wasan gaban Manchester City a fafutikar neman zama wanda zai fi zura kwallo a kakar bana.

Bayan zura kwallo 15 a kakar ta bana, Salah ne kuma ke kan gaba wurin taimakawa a zura kwallo, inda bayan wasan na ranar Lahadi, yanzu ya taimaka an zura kwallo 11 ke nan a wasannin da ya bugawa kungiyar a kakar bana.

Dan wasan na Masar yanzu ya kama hanyar maimaita nasarar da ya samu a shekarar 2022, inda ya zama wanda ya fi zura kwallo, sannan ya fi taimakawa a zura kwallo kuma duk da cewa ana ta kwan-gaba-kwan-baya a game da makomar dan wasan – kwantiraginsa zai kare a bana – har yanzu yana ci gaba da nuna bajinta.

Amma yaya za a kwatanta dan wasan mai shekara 32 da sauran zakarun ‘yan wasan da suka buga wasa a gasar ta Premier League ta Ingila?

 

Labarai Masu Nasaba

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro

Makon kafa tarihi

Salah ya fara kakar bana da kafar dama, inda ya zura kwallo 12 a wasa 12 da suka gabata yanzu ya zura kwallo 18, sannan ya taimaka an zura 15, kenan yana da hannu a kwallaye 33, hudu ke nan a gaba da duk wani dan wasa a manyan gasannin Turai.

 

A wasan Liverpool da Tottenham ya kafa tarihi uku.

Ya zama dan wasa na farko da ya haura sa hannu a zura kwallo, wato zura kwallo da taimakawa a zura sama da goma kafin Kirsimeti.

Na farko da ya taimaka a zura kwallo sama da 10 a kaka hudu a jere. Wannan ce kaka ta shida da Salah ya samu wannan nasarar, inda ya doke tsohon dan wasan Manchester United Wayne Rooney.

Yanzu Salah zai so ya kafa wani tarihin a wannan kakar, inda yanzu ya mayar da hankalinsa kan lashe takalmin zinare na wanda ya fi zura kwallaye a kaka hudu- nasarar da tsohon dan wasan Arsenal Thierry Henry ya taba yi a baya.

Salah ya zura kwallo 18 a duk kakar da ya buga a Liberpool kuma saura kwallo biyar ya zama dan wasa na biyar da ya taba zura kwallo 20 a kaka biyar, sannan dan wasan gaban na Liberpool yanzu yana fafatawa ne da Haaland domin lashe takalmin zinare.

Dan wasan na Norway ya zura kwallo 27 a kakar bara, sannan ya zura kwallo 36 a kaka biyu da ta gabata, inda ya zama dan wasa na farko tun bayan Harry Kane na Tottenham da ya lashe kambun wanda ya fi zura kwallo a kaka biyu a jere.

 

Shi ma dai Haaland yana so ya lashe kambun a bana, inda yanzu haka shi ma ya zura kwallo 10, amma halin da kungiyar ta Manchester City karkashin jagorancin Pep Guardiola ya sa ana ganin abu ne mai wahala ya lashe gasar.

Yanzu dai babu shakka Salah na cikin gwarazan ‘yan wasan Liberpool, inda ya lashe duk wani kofi da ake bukata a kungiyar kuma shi ne na hudu a cikin wadanda suka fi zura kwallaye a kungiyar, inda yake da kwallo 229 a wasanni 373, kuma yake bukatar kwallo 12 domin kamo Gordon Hodgson.

Roger Hunt na da kwallo 285, Ian Rush na da 346, wadanda sun masa nisa, amma idan zai iya ci gaba da zura kwallo kamar yadda yake yi a yanzu, zai bukaci wasanni 190 kafin ya zarce su, wanda abu ne mai wahala sosai.

A bangaren gwarazan gasar Premier League, yanzu haka Salah na cikin gwanayen ‘yan wasan gasar, inda yake da kwallo 172, kuma shi ne na takwas a jerin wadanda suka fi zura kwallo, har ila yau saura kwallo 15 Salah ya kamo na hudu Andrew Cole – wanda zai iya kamowa a karshen kakar bana.

A wasan na ranar Lahadi, Salah ya kamo Dabid Becham wajen taimakawa a zura kwallo 80, inda yanzu su biyun suke mataki na 10. Yanzu yana bukatar taimakawa a zura kwallo 34 domin kamo Kebin de Bruyne, wanda shi ne biyu.

Wanda ya fi taimakawa a zura kwallo a gasar Premier League shi ne Ryan Giggs, wanda ya taimaka aka zura kwallo 162, amma ya fi Salah buga wasa da wasanni 353 kuma idan aka hada zura kwallo da taimakawa, Salah na gaba da shi. Ya sa hannu a zura kwallo 252 a wasa 279 a gasar Premier League, inda ya zama na bakwai a jerin wadanda jimillar zurawa da taimakawa a zura kwallo kuma idan ya ci gaba da yadda yake a yanzu, Salah zai kamo Alan Shearer a jimillar zurawa da taimakawa a zura, wato guda 324.

Yanzu dai abin da ake jira a gani shi ne, shin zai iya sabunta kwantiraginsa a kungiyar ta Liberpool? Kwantiraginsa dai zai kare ne a karshen wannan kakar kuma tuni kungiyoyi daga kasar Saudiyya suka fara bibiyarsa domin ganin ya koma can da buga wasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Firaministan Malaysia: Sin Aminiyar Kasar Malaysia Ce Ta Hakika

Next Post

Ƴansanda Sun Kama Mutane 859, Sun Kwato Makamai 27 Da Alburusai 115 A Filato

Related

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

1 day ago
Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro
Wasanni

Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro

2 days ago
PSG Ta Yi Waje Rod Da Arsenal A Gasar Zakarun Turai 
Wasanni

PSG Ta Yi Waje Rod Da Arsenal A Gasar Zakarun Turai 

2 days ago
UEFA: Inter Milan Ta Yi Wa Barcelona Kancal
Wasanni

UEFA: An Kai Ruwa Rana Yayin Da Inter Ta Koro Barcelona Gida

3 days ago
Shekaru 15, Wasanni 578, Daga Karshe Harry Kane Ya Lashe Kofi
Wasanni

Shekaru 15, Wasanni 578, Daga Karshe Harry Kane Ya Lashe Kofi

5 days ago
Mun Fara Shirin Lashe Firimiya Ta Gaba –Slot
Wasanni

Mun Fara Shirin Lashe Firimiya Ta Gaba –Slot

6 days ago
Next Post
Ƴansanda Sun Kama Mutane 859, Sun Kwato Makamai 27 Da Alburusai 115 A Filato

Ƴansanda Sun Kama Mutane 859, Sun Kwato Makamai 27 Da Alburusai 115 A Filato

LABARAI MASU NASABA

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

May 10, 2025
Mambobin APC Sun Buƙaci EFCC Ta Sake Buɗe Binciken Matawalle

Mambobin APC Sun Buƙaci EFCC Ta Sake Buɗe Binciken Matawalle

May 10, 2025
Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya

Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya

May 10, 2025
Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

May 9, 2025
Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

May 9, 2025
Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

May 9, 2025
Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

May 9, 2025
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.