ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muhammad Salah: Gwarzon Afirka A Firimiyar Ingila

by Abba Ibrahim Wada and Sulaiman
1 year ago
Muhammad Salah

Kawo yanzu dai babu wani dan wasa da yake nuna bajinta daga nahiyar Afirka a gasar Firimiya kamar dan wasa Muhammad Salah na kasar Masar wanda yake buga wasa a kungiyar kwallon kafa ta Liverpool domin kusan duk mako sai ya nuna bajinta. Dan wasan gaban na Liverpool ya zura kwallo biyu a wasan da kungiyar ta lallasa Tottenham da ci shida da uku kuma da wannan nasarar ce Salah ya haura dan wasan gaban Manchester City a fafutikar neman zama wanda zai fi zura kwallo a kakar bana.

Bayan zura kwallo 15 a kakar ta bana, Salah ne kuma ke kan gaba wurin taimakawa a zura kwallo, inda bayan wasan na ranar Lahadi, yanzu ya taimaka an zura kwallo 11 ke nan a wasannin da ya bugawa kungiyar a kakar bana.

Dan wasan na Masar yanzu ya kama hanyar maimaita nasarar da ya samu a shekarar 2022, inda ya zama wanda ya fi zura kwallo, sannan ya fi taimakawa a zura kwallo kuma duk da cewa ana ta kwan-gaba-kwan-baya a game da makomar dan wasan – kwantiraginsa zai kare a bana – har yanzu yana ci gaba da nuna bajinta.

ADVERTISEMENT

Amma yaya za a kwatanta dan wasan mai shekara 32 da sauran zakarun ‘yan wasan da suka buga wasa a gasar ta Premier League ta Ingila?

 

LABARAI MASU NASABA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

Makon kafa tarihi

Salah ya fara kakar bana da kafar dama, inda ya zura kwallo 12 a wasa 12 da suka gabata yanzu ya zura kwallo 18, sannan ya taimaka an zura 15, kenan yana da hannu a kwallaye 33, hudu ke nan a gaba da duk wani dan wasa a manyan gasannin Turai.

 

A wasan Liverpool da Tottenham ya kafa tarihi uku.

Ya zama dan wasa na farko da ya haura sa hannu a zura kwallo, wato zura kwallo da taimakawa a zura sama da goma kafin Kirsimeti.

Na farko da ya taimaka a zura kwallo sama da 10 a kaka hudu a jere. Wannan ce kaka ta shida da Salah ya samu wannan nasarar, inda ya doke tsohon dan wasan Manchester United Wayne Rooney.

Yanzu Salah zai so ya kafa wani tarihin a wannan kakar, inda yanzu ya mayar da hankalinsa kan lashe takalmin zinare na wanda ya fi zura kwallaye a kaka hudu- nasarar da tsohon dan wasan Arsenal Thierry Henry ya taba yi a baya.

Salah ya zura kwallo 18 a duk kakar da ya buga a Liberpool kuma saura kwallo biyar ya zama dan wasa na biyar da ya taba zura kwallo 20 a kaka biyar, sannan dan wasan gaban na Liberpool yanzu yana fafatawa ne da Haaland domin lashe takalmin zinare.

Dan wasan na Norway ya zura kwallo 27 a kakar bara, sannan ya zura kwallo 36 a kaka biyu da ta gabata, inda ya zama dan wasa na farko tun bayan Harry Kane na Tottenham da ya lashe kambun wanda ya fi zura kwallo a kaka biyu a jere.

 

Shi ma dai Haaland yana so ya lashe kambun a bana, inda yanzu haka shi ma ya zura kwallo 10, amma halin da kungiyar ta Manchester City karkashin jagorancin Pep Guardiola ya sa ana ganin abu ne mai wahala ya lashe gasar.

Yanzu dai babu shakka Salah na cikin gwarazan ‘yan wasan Liberpool, inda ya lashe duk wani kofi da ake bukata a kungiyar kuma shi ne na hudu a cikin wadanda suka fi zura kwallaye a kungiyar, inda yake da kwallo 229 a wasanni 373, kuma yake bukatar kwallo 12 domin kamo Gordon Hodgson.

Roger Hunt na da kwallo 285, Ian Rush na da 346, wadanda sun masa nisa, amma idan zai iya ci gaba da zura kwallo kamar yadda yake yi a yanzu, zai bukaci wasanni 190 kafin ya zarce su, wanda abu ne mai wahala sosai.

A bangaren gwarazan gasar Premier League, yanzu haka Salah na cikin gwanayen ‘yan wasan gasar, inda yake da kwallo 172, kuma shi ne na takwas a jerin wadanda suka fi zura kwallo, har ila yau saura kwallo 15 Salah ya kamo na hudu Andrew Cole – wanda zai iya kamowa a karshen kakar bana.

A wasan na ranar Lahadi, Salah ya kamo Dabid Becham wajen taimakawa a zura kwallo 80, inda yanzu su biyun suke mataki na 10. Yanzu yana bukatar taimakawa a zura kwallo 34 domin kamo Kebin de Bruyne, wanda shi ne biyu.

Wanda ya fi taimakawa a zura kwallo a gasar Premier League shi ne Ryan Giggs, wanda ya taimaka aka zura kwallo 162, amma ya fi Salah buga wasa da wasanni 353 kuma idan aka hada zura kwallo da taimakawa, Salah na gaba da shi. Ya sa hannu a zura kwallo 252 a wasa 279 a gasar Premier League, inda ya zama na bakwai a jerin wadanda jimillar zurawa da taimakawa a zura kwallo kuma idan ya ci gaba da yadda yake a yanzu, Salah zai kamo Alan Shearer a jimillar zurawa da taimakawa a zura, wato guda 324.

Yanzu dai abin da ake jira a gani shi ne, shin zai iya sabunta kwantiraginsa a kungiyar ta Liberpool? Kwantiraginsa dai zai kare ne a karshen wannan kakar kuma tuni kungiyoyi daga kasar Saudiyya suka fara bibiyarsa domin ganin ya koma can da buga wasa.

Muhammad Salah
Abba Ibrahim Wada
Website |  + posts Bio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?
Muhammad Salah
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

MASU ALAKA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
Next Post
Ƴansanda Sun Kama Mutane 859, Sun Kwato Makamai 27 Da Alburusai 115 A Filato

Ƴansanda Sun Kama Mutane 859, Sun Kwato Makamai 27 Da Alburusai 115 A Filato

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.