• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muhimman Abubuwan Da Suka Faru Sakamakon Zanga-Zangar Da Ta Barke A Isra’ila

by Ammar Muhammad
2 years ago
in Labarai
0
Muhimman Abubuwan Da Suka Faru Sakamakon Zanga-Zangar Da Ta Barke A Isra’ila
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An shiga mako na 12 ke nan ana tafka zanga-zanga a kasar Isra’ila. Dubban daruruwa mutane ne ke sake fitowa a kowacce rana suna shiga sahun masu zanga-zangar tare da yin Allah-wadai da gwamnantin Benjamin Netanyahu bisa bullo da dokar kwace ikon bangaren shari’a.

Zanga-zangar wacce tunda farko ta soma da mutane kalilan ta fara ci kamar wutar daji a kasar ganin yadda ta soma karbuwa a wurin wasu jami’an gwamnati da ma’aikata da suke adawa da sabuwar dokar da Firaministan kasar Benjamin Netanyahu ya bullo da shi.

Rahotanni daga kafafen watsa labaran kasar sun tabbatarda cewa ya zuwa yanzu muhimman abubuwa sun faru daga farkon zanga-zangar zuwa hada wannan rahoton.

Abubuwan da suka faru sune kamar haka;

  1. An rufe kafatanin gidajen abinci, cibiyoyin lafiya, ofisoshin gwamnati, ma’aikatar kudi, Babban Bankin kasar Isra’ila, tasoshin zirga-zirga da na ababen hawa, an kulle jami’o’in kasar, wuraren tarihi, shagunan sayayya, da sauran muhimman wurare.
  2.  Dukkanin ma’aikatan wadannan wurare sun tafi yajin aiki tare da shiga cikin zanga-zangar da take ci gaba da kazancewa a Haramtacciyar kasar ta Isra’ila.
  3.  An rufe ofishin Jakadancin Isra’ila da ke birnin Washington da wasu wuraren hulda da Isra’ila da ke Amurka domin nuna goyon baya ga masu zanga-zangar.
  4. Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, yana yi wa masu zanga-zangar barazanar shekar da jinanensu ta hanyar shirin jami’an ko ta kwana. Inda jami’an ke antaya wa masu zanga-zangar ruwan zafi da barkonon tsohuwa tare da dukan masu zanga-zangar.
  5.  Masu zanga-zangar na kara yawa a kowacce rana inda bayanai ke tabbatar da cewa dubban daruruwa ne a yanzu ke kira da gwamnatin Netanyahu da ta janye kudurin dokarta, idan ba haka ba za su ci gaba da zanga-zangar har sai mama ta gani.
  6.  Masu zanga-zangar na zuwa muhimman wurare a Isra’ila suna shigar da kokensu. A inda suka je har kotun kolin kasar. Zanga-zangar har wala yau ta karade har cikin babbar kasar na TelAbib.
  7. Kungiyar kwadago mafi girma a kasar ta tafi yajin aiki na kafatanin ma’aikata inda ta bukace su da su tafi yajin aiki da kuma shiga cikin masu zanga-zangar.
  8. Fiye da shugabannin garuruwa 24 ne suka tafi yajin aikin cin abinci domin tursasawa gwamnatin Netanyahu.
  9. Asaf Zamir, wanda shi ne Babban Jami’in lura da ofishin Jakadancin Isra’ila na birnin New York ya ajiye aikinsa a wani mataki na goyon bayan masu zanga-zanga tare da Allah-wadai da gwamnatin Netanyahu bisa korar ministan tsaron kasar.
  10. Ministan kudin Isra’ila cikin firgici ya ce dole ne Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu ya saurari koken masu zanga-zangar. Inda ya goyi bayan masu zanga-zangar tare da yin kira da masu zanga-zangar su yi tururuwa a birnin Jerusalem. Wannan furuci na sa ya sanya Firaministan kasar Isra’ila, ya sauke ministan tsaron.
  11.  Shugaba Biden na kasar Amurka ya ce dole ne hukumomi a Isra’ila su yi takatsantsan tare da yin sulhu da masu zanga-zangar.
  12. Sai dai sakamakon yadda zanga-zangar kullum take kara tumbatsa a kasar, tare da barbazuwa a sassan kasar daban-daban da kuma matsin lamba da Firaminista Netanyahu ke fuskanta daga ‘yan adawa da jami’an kasar, ya tilasta masa jinkirta kudurin dokar sake yi wa bangaren shari’ar garambawul.

Sai dai masu zanga-zangar sun ce ba jinkirtawa suka bukata daga gare shi ba illa iyaka ya dakatar da kudurin dokar baki daya.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yanke Wa Wasu ‘Yan China 2 Hukuncin Daurin Shekaru 12 A Sakkwato

Next Post

Sabbin Zababbun Gwamnoni Na Bisa Tsinin Mashi

Related

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano
Labarai

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

26 minutes ago
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

1 hour ago
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

5 hours ago
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace
Labarai

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

6 hours ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

15 hours ago
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta
Labarai

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

17 hours ago
Next Post
Nijeriya

Sabbin Zababbun Gwamnoni Na Bisa Tsinin Mashi

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.