• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muhimman Abubuwan Da Suka Faru Sakamakon Zanga-Zangar Da Ta Barke A Isra’ila

by Ammar Muhammad
2 years ago
in Labarai
0
Muhimman Abubuwan Da Suka Faru Sakamakon Zanga-Zangar Da Ta Barke A Isra’ila
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An shiga mako na 12 ke nan ana tafka zanga-zanga a kasar Isra’ila. Dubban daruruwa mutane ne ke sake fitowa a kowacce rana suna shiga sahun masu zanga-zangar tare da yin Allah-wadai da gwamnantin Benjamin Netanyahu bisa bullo da dokar kwace ikon bangaren shari’a.

Zanga-zangar wacce tunda farko ta soma da mutane kalilan ta fara ci kamar wutar daji a kasar ganin yadda ta soma karbuwa a wurin wasu jami’an gwamnati da ma’aikata da suke adawa da sabuwar dokar da Firaministan kasar Benjamin Netanyahu ya bullo da shi.

Rahotanni daga kafafen watsa labaran kasar sun tabbatarda cewa ya zuwa yanzu muhimman abubuwa sun faru daga farkon zanga-zangar zuwa hada wannan rahoton.

Abubuwan da suka faru sune kamar haka;

  1. An rufe kafatanin gidajen abinci, cibiyoyin lafiya, ofisoshin gwamnati, ma’aikatar kudi, Babban Bankin kasar Isra’ila, tasoshin zirga-zirga da na ababen hawa, an kulle jami’o’in kasar, wuraren tarihi, shagunan sayayya, da sauran muhimman wurare.
  2.  Dukkanin ma’aikatan wadannan wurare sun tafi yajin aiki tare da shiga cikin zanga-zangar da take ci gaba da kazancewa a Haramtacciyar kasar ta Isra’ila.
  3.  An rufe ofishin Jakadancin Isra’ila da ke birnin Washington da wasu wuraren hulda da Isra’ila da ke Amurka domin nuna goyon baya ga masu zanga-zangar.
  4. Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, yana yi wa masu zanga-zangar barazanar shekar da jinanensu ta hanyar shirin jami’an ko ta kwana. Inda jami’an ke antaya wa masu zanga-zangar ruwan zafi da barkonon tsohuwa tare da dukan masu zanga-zangar.
  5.  Masu zanga-zangar na kara yawa a kowacce rana inda bayanai ke tabbatar da cewa dubban daruruwa ne a yanzu ke kira da gwamnatin Netanyahu da ta janye kudurin dokarta, idan ba haka ba za su ci gaba da zanga-zangar har sai mama ta gani.
  6.  Masu zanga-zangar na zuwa muhimman wurare a Isra’ila suna shigar da kokensu. A inda suka je har kotun kolin kasar. Zanga-zangar har wala yau ta karade har cikin babbar kasar na TelAbib.
  7. Kungiyar kwadago mafi girma a kasar ta tafi yajin aiki na kafatanin ma’aikata inda ta bukace su da su tafi yajin aiki da kuma shiga cikin masu zanga-zangar.
  8. Fiye da shugabannin garuruwa 24 ne suka tafi yajin aikin cin abinci domin tursasawa gwamnatin Netanyahu.
  9. Asaf Zamir, wanda shi ne Babban Jami’in lura da ofishin Jakadancin Isra’ila na birnin New York ya ajiye aikinsa a wani mataki na goyon bayan masu zanga-zanga tare da Allah-wadai da gwamnatin Netanyahu bisa korar ministan tsaron kasar.
  10. Ministan kudin Isra’ila cikin firgici ya ce dole ne Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu ya saurari koken masu zanga-zangar. Inda ya goyi bayan masu zanga-zangar tare da yin kira da masu zanga-zangar su yi tururuwa a birnin Jerusalem. Wannan furuci na sa ya sanya Firaministan kasar Isra’ila, ya sauke ministan tsaron.
  11.  Shugaba Biden na kasar Amurka ya ce dole ne hukumomi a Isra’ila su yi takatsantsan tare da yin sulhu da masu zanga-zangar.
  12. Sai dai sakamakon yadda zanga-zangar kullum take kara tumbatsa a kasar, tare da barbazuwa a sassan kasar daban-daban da kuma matsin lamba da Firaminista Netanyahu ke fuskanta daga ‘yan adawa da jami’an kasar, ya tilasta masa jinkirta kudurin dokar sake yi wa bangaren shari’ar garambawul.

Sai dai masu zanga-zangar sun ce ba jinkirtawa suka bukata daga gare shi ba illa iyaka ya dakatar da kudurin dokar baki daya.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda A Kano Sun GargaÉ—i Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yanke Wa Wasu ‘Yan China 2 Hukuncin Daurin Shekaru 12 A Sakkwato

Next Post

Sabbin Zababbun Gwamnoni Na Bisa Tsinin Mashi

Related

Sanusi
Manyan Labarai

‘Yansanda A Kano Sun GargaÉ—i Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

9 hours ago
Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 
Labarai

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

12 hours ago
Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

13 hours ago
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus
Manyan Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

15 hours ago
Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
Manyan Labarai

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

18 hours ago
Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet
Manyan Labarai

Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet

19 hours ago
Next Post
Nijeriya

Sabbin Zababbun Gwamnoni Na Bisa Tsinin Mashi

LABARAI MASU NASABA

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

June 3, 2025
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

June 3, 2025
Sanusi

‘Yansanda A Kano Sun GargaÉ—i Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

June 3, 2025
Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

June 3, 2025
An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

June 3, 2025
Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

June 3, 2025
Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

June 3, 2025
Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.