• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mukaddashiyar Shugabar NIS Ta Ayyana Dokar Ta-baci Kan Ayyukan Fasfo

by Abdulrazaq Yahuza
2 years ago
in Labarai, Kananan Labarai
0
Mukaddashiyar Shugabar NIS Ta Ayyana Dokar Ta-baci Kan Ayyukan Fasfo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mukaddashiyar Kwanturola Janar ta Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS), Caroline Wura-Ola Adepoju, ta sanar da kafa dokar ta-baci kan batutuwan da suka shafi fasfo a kasar nan.

Ta bayyana hakan ne a ziyarar aiki da ta kai jihar Legas a ranar 15 ga watan Yuni 2023, inda ta jaddada bukatar gaggawa ta magance kalubalen da ‘yan Nijeriya ke fuskanta wajen samun fasfo tare da ayyana cikakken shirin daukar matakin da ya dace domin tunkarar wadannan matsaloli yadda ya kamata.

Ziyarar ta Ag CGI a Legas ta kunshi nazarin muhimman al’amura da suka shafi gyara matsalar Fasfo. Ta kuma kaddamar da wani katafaren ofishin biza na zamani a babban zauren isowar baki a filin tashi da saukar jiragen sama na Murtala Mohammed, inda ta nuna kudirinta na inganta harkokin shige da fice baki daya ga masu shigowa Nijeriya. Bayan haka ta kai ziyarar bazata zuwa ofishin fasfo na Alausa domin gane wa idonta halin da ake ciki.

NIS

A cikin jawabinta, Ag. CGI Adepoju ta jaddada wajabcin wargaza duk wasu abubuwa da ke kawo cikas wajen neman Fasfo. Ta kuma jaddada cewa, manyan jami’an NIS sun himmatu sosai wajen magance matsalolin da suka shafi fasaha don tabbatar da samar da ingantaccen aiki ga jama’a.

Labarai Masu Nasaba

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

Bisa la’akari da muhimmancin wayar da kan jama’a game da sauran masu ruwa da tsaki musamman sarakunan gargajiya, mukaddashiyar shugabar ta NIS ta fara wannan yunkurin ne da wata ziyara da ta kai wa Sarkin Legas, Oba Rilwan Akiolu, inda ta nemi hadin kan sarakunan gargajiya wajen wayar da kan jama’a game da illolin da ke tattare da safarar mutane da kuma kaddamar da hadin gwiwar yaki da wannan matsala.

NIS

Dokar ta-baci kan batutuwan fasfo na nuni da sabon alkawarin da NIS ta yi na magance kalubalen da ‘yan Nijeriya ke fuskanta na neman fasfo.

Idan za a yi tunawa, Ag. CGI Adepoju kwanan baya ta umurci dukkan jami’an da ke kula da fasfo, da sassan da abin ya shafa da kuma ma’aikatan NIS ciki har da Ofishoshin Jakadancin Nijeriya a kasashen waje, da su yi aiki tukuru domin kawar da duk wani cikas da ke hana ‘yan Nijeriya samun fasfo cikin gaggawa. Hukumar NIS tana yin amfani da fasaha tare da ƙaddamar da ingantattun matakan gudanarwa don haɓaka aikace-aikacen Fasfo da tsarin bayarwa.

NIS

Mukaddashiyar shugabar ta bukaci daukacin ‘yan Nijeriya da su ci gaba da hakuri tare da bayar da hadin kai ga hukumar ta NIS yayin da take daukar kwararan matakai don magance matsalar Fasfo. Ta kuma tabbatar wa da jama’a cewa ana kokarin ganin duk wani dan Nijeriya da ya cancanta ya samu Fasfo a kan lokaci.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AikiFasfoNISZiyara
ShareTweetSendShare
Previous Post

NIS Reshen Ribas Ta Bukaci Mutunta Umarnin Bangaren Zartarwa Kan Aikin Yi Ga ‘Yan Kasa

Next Post

Hidimar Da Daular Sakkwato Ke Yi Wajen Buga Miliyoyin Littafai – Sarkin Musulmi

Related

Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

1 hour ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

3 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

4 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

5 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

6 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

8 hours ago
Next Post
Hidimar Da Daular Sakkwato Ke Yi Wajen Buga Miliyoyin Littafai – Sarkin Musulmi

Hidimar Da Daular Sakkwato Ke Yi Wajen Buga Miliyoyin Littafai - Sarkin Musulmi

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.