• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mukaddashiyar Shugabar NIS Ta Ayyana Dokar Ta-baci Kan Ayyukan Fasfo

by Abdulrazaq Yahuza
2 years ago
in Labarai, Kananan Labarai
0
Mukaddashiyar Shugabar NIS Ta Ayyana Dokar Ta-baci Kan Ayyukan Fasfo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mukaddashiyar Kwanturola Janar ta Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS), Caroline Wura-Ola Adepoju, ta sanar da kafa dokar ta-baci kan batutuwan da suka shafi fasfo a kasar nan.

Ta bayyana hakan ne a ziyarar aiki da ta kai jihar Legas a ranar 15 ga watan Yuni 2023, inda ta jaddada bukatar gaggawa ta magance kalubalen da ‘yan Nijeriya ke fuskanta wajen samun fasfo tare da ayyana cikakken shirin daukar matakin da ya dace domin tunkarar wadannan matsaloli yadda ya kamata.

Ziyarar ta Ag CGI a Legas ta kunshi nazarin muhimman al’amura da suka shafi gyara matsalar Fasfo. Ta kuma kaddamar da wani katafaren ofishin biza na zamani a babban zauren isowar baki a filin tashi da saukar jiragen sama na Murtala Mohammed, inda ta nuna kudirinta na inganta harkokin shige da fice baki daya ga masu shigowa Nijeriya. Bayan haka ta kai ziyarar bazata zuwa ofishin fasfo na Alausa domin gane wa idonta halin da ake ciki.

NIS

A cikin jawabinta, Ag. CGI Adepoju ta jaddada wajabcin wargaza duk wasu abubuwa da ke kawo cikas wajen neman Fasfo. Ta kuma jaddada cewa, manyan jami’an NIS sun himmatu sosai wajen magance matsalolin da suka shafi fasaha don tabbatar da samar da ingantaccen aiki ga jama’a.

Labarai Masu Nasaba

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Bisa la’akari da muhimmancin wayar da kan jama’a game da sauran masu ruwa da tsaki musamman sarakunan gargajiya, mukaddashiyar shugabar ta NIS ta fara wannan yunkurin ne da wata ziyara da ta kai wa Sarkin Legas, Oba Rilwan Akiolu, inda ta nemi hadin kan sarakunan gargajiya wajen wayar da kan jama’a game da illolin da ke tattare da safarar mutane da kuma kaddamar da hadin gwiwar yaki da wannan matsala.

NIS

Dokar ta-baci kan batutuwan fasfo na nuni da sabon alkawarin da NIS ta yi na magance kalubalen da ‘yan Nijeriya ke fuskanta na neman fasfo.

Idan za a yi tunawa, Ag. CGI Adepoju kwanan baya ta umurci dukkan jami’an da ke kula da fasfo, da sassan da abin ya shafa da kuma ma’aikatan NIS ciki har da Ofishoshin Jakadancin Nijeriya a kasashen waje, da su yi aiki tukuru domin kawar da duk wani cikas da ke hana ‘yan Nijeriya samun fasfo cikin gaggawa. Hukumar NIS tana yin amfani da fasaha tare da ƙaddamar da ingantattun matakan gudanarwa don haɓaka aikace-aikacen Fasfo da tsarin bayarwa.

NIS

Mukaddashiyar shugabar ta bukaci daukacin ‘yan Nijeriya da su ci gaba da hakuri tare da bayar da hadin kai ga hukumar ta NIS yayin da take daukar kwararan matakai don magance matsalar Fasfo. Ta kuma tabbatar wa da jama’a cewa ana kokarin ganin duk wani dan Nijeriya da ya cancanta ya samu Fasfo a kan lokaci.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AikiFasfoNISZiyara
ShareTweetSendShare
Previous Post

NIS Reshen Ribas Ta Bukaci Mutunta Umarnin Bangaren Zartarwa Kan Aikin Yi Ga ‘Yan Kasa

Next Post

Hidimar Da Daular Sakkwato Ke Yi Wajen Buga Miliyoyin Littafai – Sarkin Musulmi

Related

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka
Ra'ayi Riga

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

41 minutes ago
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata
Labarai

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

2 hours ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

5 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

7 hours ago
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa
Labarai

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

8 hours ago
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

9 hours ago
Next Post
Hidimar Da Daular Sakkwato Ke Yi Wajen Buga Miliyoyin Littafai – Sarkin Musulmi

Hidimar Da Daular Sakkwato Ke Yi Wajen Buga Miliyoyin Littafai - Sarkin Musulmi

LABARAI MASU NASABA

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.