• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mukaddashiyar Shugabar NIS Ta Ayyana Dokar Ta-baci Kan Ayyukan Fasfo

by Abdulrazaq Yahuza
2 years ago
in Labarai, Kananan Labarai
0
Mukaddashiyar Shugabar NIS Ta Ayyana Dokar Ta-baci Kan Ayyukan Fasfo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mukaddashiyar Kwanturola Janar ta Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS), Caroline Wura-Ola Adepoju, ta sanar da kafa dokar ta-baci kan batutuwan da suka shafi fasfo a kasar nan.

Ta bayyana hakan ne a ziyarar aiki da ta kai jihar Legas a ranar 15 ga watan Yuni 2023, inda ta jaddada bukatar gaggawa ta magance kalubalen da ‘yan Nijeriya ke fuskanta wajen samun fasfo tare da ayyana cikakken shirin daukar matakin da ya dace domin tunkarar wadannan matsaloli yadda ya kamata.

Ziyarar ta Ag CGI a Legas ta kunshi nazarin muhimman al’amura da suka shafi gyara matsalar Fasfo. Ta kuma kaddamar da wani katafaren ofishin biza na zamani a babban zauren isowar baki a filin tashi da saukar jiragen sama na Murtala Mohammed, inda ta nuna kudirinta na inganta harkokin shige da fice baki daya ga masu shigowa Nijeriya. Bayan haka ta kai ziyarar bazata zuwa ofishin fasfo na Alausa domin gane wa idonta halin da ake ciki.

NIS

A cikin jawabinta, Ag. CGI Adepoju ta jaddada wajabcin wargaza duk wasu abubuwa da ke kawo cikas wajen neman Fasfo. Ta kuma jaddada cewa, manyan jami’an NIS sun himmatu sosai wajen magance matsalolin da suka shafi fasaha don tabbatar da samar da ingantaccen aiki ga jama’a.

Labarai Masu Nasaba

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bisa la’akari da muhimmancin wayar da kan jama’a game da sauran masu ruwa da tsaki musamman sarakunan gargajiya, mukaddashiyar shugabar ta NIS ta fara wannan yunkurin ne da wata ziyara da ta kai wa Sarkin Legas, Oba Rilwan Akiolu, inda ta nemi hadin kan sarakunan gargajiya wajen wayar da kan jama’a game da illolin da ke tattare da safarar mutane da kuma kaddamar da hadin gwiwar yaki da wannan matsala.

NIS

Dokar ta-baci kan batutuwan fasfo na nuni da sabon alkawarin da NIS ta yi na magance kalubalen da ‘yan Nijeriya ke fuskanta na neman fasfo.

Idan za a yi tunawa, Ag. CGI Adepoju kwanan baya ta umurci dukkan jami’an da ke kula da fasfo, da sassan da abin ya shafa da kuma ma’aikatan NIS ciki har da Ofishoshin Jakadancin Nijeriya a kasashen waje, da su yi aiki tukuru domin kawar da duk wani cikas da ke hana ‘yan Nijeriya samun fasfo cikin gaggawa. Hukumar NIS tana yin amfani da fasaha tare da ƙaddamar da ingantattun matakan gudanarwa don haɓaka aikace-aikacen Fasfo da tsarin bayarwa.

NIS

Mukaddashiyar shugabar ta bukaci daukacin ‘yan Nijeriya da su ci gaba da hakuri tare da bayar da hadin kai ga hukumar ta NIS yayin da take daukar kwararan matakai don magance matsalar Fasfo. Ta kuma tabbatar wa da jama’a cewa ana kokarin ganin duk wani dan Nijeriya da ya cancanta ya samu Fasfo a kan lokaci.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AikiFasfoNISZiyara
ShareTweetSendShare
Previous Post

NIS Reshen Ribas Ta Bukaci Mutunta Umarnin Bangaren Zartarwa Kan Aikin Yi Ga ‘Yan Kasa

Next Post

Hidimar Da Daular Sakkwato Ke Yi Wajen Buga Miliyoyin Littafai – Sarkin Musulmi

Related

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano
Labarai

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

5 hours ago
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Manyan Labarai

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

7 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta MiÆ™a SaÆ™on Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan ÆŠantata Na Madina
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta MiÆ™a SaÆ™on Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan ÆŠantata Na Madina

7 hours ago
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara
Manyan Labarai

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

9 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar ÆŠantata
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar ÆŠantata

14 hours ago
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

15 hours ago
Next Post
Hidimar Da Daular Sakkwato Ke Yi Wajen Buga Miliyoyin Littafai – Sarkin Musulmi

Hidimar Da Daular Sakkwato Ke Yi Wajen Buga Miliyoyin Littafai - Sarkin Musulmi

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta MiÆ™a SaÆ™on Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan ÆŠantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta MiÆ™a SaÆ™on Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan ÆŠantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.