• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Karbi Rancen Dala Biliyan 1 Don Tallafa Wa Matatar Man Dangote —NNPC

by Bello Hamza and Sulaiman
6 months ago
in Labarai
0
NNPCL
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamfanin man fetur na Nijeriya (NNPCL) ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ta hannun kamfanin ta karbo rancen dala biliyan daya domin tallafa wa aikin matatar man Dangote a lokacin da ta fuskanci wasu matsaloli na kudi.

 

Babban jami’in yada labarai na kamfanin NNPC, Olufemi Soneye, ne ya bayyana hakan a lokacin da yake jawabi a taron masu ruwa da tsaki kan harkokin makamashi a Abuja.

  • Kasar Sin Na Adawa Da Danne Kamfanoninta Da Amurka Take Yi Bisa Fakewa Da Batun Tsaron Kasa
  • Shugaban Sin Ya Jinjinawa Nasarorin Da Yankin Macao Ya Samu Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata

Da yake karin haske kan nasarorin da babban kamfanin mai na kasa a karkashin jagorancin Malam Mele Kyari ya samu, Sonoye ya ce, “ A karkashin jagorancin Mele Kyari mai hangen nesa, kamfanin NNPC Ltd ya samu nasarori masu ywa, inda ya sake fayyace yadda harkar man fetur da iskar gas ta Nijeriya ke tafiya.

 

Labarai Masu Nasaba

Kashim Shettima Ya Ƙaddamar Da Shirin Gyaran Kayayyakin Gwamnati A Borno

Gwamnatin Kano Ta Nemi Diyya Daga Gwamnatin Tarayya Kan Soke Hawan Sallah

“Sake bude matatar man ta Fatakwal ya nuna wani gagarumin sauyi a yunkurin Nijeriya na samun wadatar makamashi, yana mai jaddada aniyar kamfanin na farfado da aikin tace man fetur a kasar nan.

 

“Haka zalika, NNPC ta yi nasarar daukar iskar Gas (CNG) a matsayin wata hanyar samar da makamashi, wanda zai bai wa ‘yan Nijeriya mafita a cikin tsadar makamashi a duniya.

 

“Shawarwari mai muhimmanci na samun lamunin dala biliyan 1 da NNPC ta goyi bayan ya taka rawar gani wajen tallafa wa matatar man Dangote a lokacin da ake fama da matsalar rashin mai, wanda ya bayar da hanyar samar da kafa matatar mai ta farko mai zaman kanta a Nijeriya. Wannan yunkurin ya nuna himma da kwazon kamfanin na NNPC na habaka hadin gwiwar jama’a da masu zaman kansu wadanda ke haifar da ci gaban kasa.

 

“A wata nasara mai cike da tarihi, NNPC, a karkashin jagorancin Kyari, ta bayyana riba a karon farko cikin shekaru da dama, wanda ke nuna gagarumin sauyin kudi. Tuni dai kamfanin ya zarce hasashen ribar da yake samu a shekarar 2024, lamarin da ke nuni da sauye-sauyen da ya aiwatar.

 

“Bugu da kari, Kyari ya saukake rancen dala biliyan 3 na Gazelle, wani muhimmin tsoma bakin da ya taimaka wajen daidaita al’amuran tarayya a lokacin da ake fama da matsalar canjin kudin waje,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wolves Ta Naɗa Vitor Pereira A Matsayin Sabon Kocinta

Next Post

Peng Liyuan Ta Ziyarci Dakin Ajiye Kayayyakin Tarihi a Yankin Macao

Related

Kashim Shettima Ya Ƙaddamar Da Shirin Gyaran Kayayyakin Gwamnati A Borno
Manyan Labarai

Kashim Shettima Ya Ƙaddamar Da Shirin Gyaran Kayayyakin Gwamnati A Borno

9 minutes ago
Gwamnatin Kano Ta Nemi Diyya Daga Gwamnatin Tarayya Kan Soke Hawan Sallah
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Nemi Diyya Daga Gwamnatin Tarayya Kan Soke Hawan Sallah

2 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

3 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

4 hours ago
Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu
Manyan Labarai

Bangarorin Sudan Da Ke Dauki Ba Dadi Sun Zargi Juna Da Kai Hari Kan Jerin Gwanon Motocin MDD

6 hours ago
An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya
Labarai

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

12 hours ago
Next Post
Peng Liyuan Ta Ziyarci Dakin Ajiye Kayayyakin Tarihi a Yankin Macao

Peng Liyuan Ta Ziyarci Dakin Ajiye Kayayyakin Tarihi a Yankin Macao

LABARAI MASU NASABA

Kashim Shettima Ya Ƙaddamar Da Shirin Gyaran Kayayyakin Gwamnati A Borno

Kashim Shettima Ya Ƙaddamar Da Shirin Gyaran Kayayyakin Gwamnati A Borno

June 8, 2025
Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar

Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar

June 8, 2025
Gwamnatin Kano Ta Nemi Diyya Daga Gwamnatin Tarayya Kan Soke Hawan Sallah

Gwamnatin Kano Ta Nemi Diyya Daga Gwamnatin Tarayya Kan Soke Hawan Sallah

June 8, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

June 8, 2025
Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 

Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 

June 8, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

June 8, 2025
Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu

Bangarorin Sudan Da Ke Dauki Ba Dadi Sun Zargi Juna Da Kai Hari Kan Jerin Gwanon Motocin MDD

June 8, 2025
Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

June 8, 2025
Bambancin Bukukuwan Sallar Bara Da Ta Bana

Bambancin Bukukuwan Sallar Bara Da Ta Bana

June 8, 2025
Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

June 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.