• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Samu Gawar Mutum 15, Shanu 2000 Sun Bace Da Kone Mana Gidaje 78 A Jihar Filato – MACBAN

by Muhammad
2 years ago
in Labarai
0
Mun Samu Gawar Mutum 15, Shanu 2000 Sun Bace Da Kone Mana Gidaje 78 A Jihar Filato – MACBAN
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) a ranar Lahadi ta ce an kashe mutane 15 bayan wani farmaki da ake zargin kai musu a karamar hukumar Mangu ta jihar Filato.

Kungiyar ta kuma ce an kona gidaje 78 na mambobinta yayin da sama da shanu 2,000 suka bace bayan farmakin.

  • Ana Ci Gaba Da Zaman Gida A Yankin Mangu Ta Jihar Filato Kan Sanya Dokar Hana Fita Na Sa’o’i 24
  • An Kashe Mutum 2, An Raunata 3 A Wani Sabon Hari A Filato

Nuru Abdullahi, shugaban kungiyar na jihar ne ya bayyana hakan ga manema labarai jiya, a Jos, babban birnin jihar.

Daily Trust ta ruwaito cewa a ranar Asabar din da ta gabata kungiyar ta zargi ‘Operation Rainbow’, jami’an tsaron jihar da kai wa yankinsu hari tare da kunna musu wuta, zargin da rundunar ta musanta.

Ya ce, “A harin da aka kai a kauyukan Mangu, mun gano gawarwaki 15 da aka kashe a ranar Juma’a. Kimanin gidaje 78 ne suka kone. Shanu da adadinsu ya kai 2,000 har yanzu ba a gansu ba. Wannan abin takaicin ne a jihar.”

Labarai Masu Nasaba

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

Abdullahi ya kuma yi zargin wani shiri na kai wa al’ummarsu hari da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne.

“Akwai rahoton sirri da ke nuna cewa akwai kwararrun ‘yan bindiga da aka dauka aka kawo su yaki tare da fatattakar duk Fulani daga jihar Filato da sunan rikici. Don haka a halin yanzu muna kira ga gwamnatin tarayya da ta gaggauta kawo karshen abin da ke faruwa a karamar hukumar Mangu.

“Ya kamata su dauki matakin gaggawa kafin al’amura su wuce gona da iri. Muna rokon Gwamnatin tarayya da ta dauki matakin da ya dace don kada al’amura su fita daga hannunsu. Ba za mu ci gaba da kallon yadda mutane ke kashe mu da lalata mana dukiyoyi ba,” Abdullahi ya kara da cewa.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Alabo Alfred, da na runduna ta uku ta rundunar sojojin Nijeriya, Rukuba Barrack, Laftanar Kanar Ishaku Sabastine Takwa, har yanzu ba su amsa kira da sakon da wakilin na Trust ya yi musi kan lamarin ba har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto.

An samu rikici a kauyukan karamar hukumar Mangu inda aka tabbatar da mutuwar mutane sama da 200 da suka hada da mata da kananan yara a watannin baya.

A halin da ake ciki gwamnan jihar Filato Caleb Mutfwang ya sanya dokar hana fita ta sa’o’i 24 a karamar hukumar Mangu don saisaita al’amura dakile asarar rayuka da dukiyoyi a yankin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FilatoFulaniJosMACBANMangu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Zama Sabon Shugaban ECOWAS

Next Post

An Kubutar Da Mutum 30 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Birnin Kebbi

Related

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara
Labarai

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

18 minutes ago
An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya
Labarai

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

12 hours ago
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba
Manyan Labarai

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

13 hours ago
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara
Labarai

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

15 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

16 hours ago
Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?
Manyan Labarai

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

16 hours ago
Next Post
An Kubutar Da Mutum 30 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Birnin Kebbi

An Kubutar Da Mutum 30 Daga Hannun 'Yan Bindiga A Birnin Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

September 15, 2025
Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

September 15, 2025
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

September 14, 2025
Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

September 14, 2025
Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

September 14, 2025
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

September 14, 2025
Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

September 14, 2025
Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.